Sura 9

1 Sai Allah ya albarkaci Nuhu da 'ya'yansa, ya ce da su, "Ku ruɓanɓanya ku hayayyafa, ku cika duniya. 2 Tsoronku da tsoratarwarku za ta zama a kan dukkan dabbobi masu rai dake duniya, da kowanne tsuntsu dake sararin sama, da duk wani abu dake motsi bisa ƙasa, da dukkan kifayen teku. An bada su a hannunka. 3 Dukkan wani abu mai motsi dake rayuwa zai zama abinci a gare ku. Na baku koren ganyayyaki, yanzu na ba ku kowanne abu. 4 Amma ba za ku ci naman da jininsa da ransa ke cikinsa ba. 5 Amma a bisa jininka, da ran dake cikin jininka, zan bukaci diyya. Daga dukkan dabbobi zan bukace ta. Daga hannun kowanne mutum, wato, mutumin da ya aikata kisan kai ga ɗan'uwansa, 6 zan bukaci bada lissafi na wannan mutum. Duk wanda ya zubar da jinin mutum ta wurin mutum za a zubar da jininsa, domin cikin kammanin Allah aka hallici mutum. 7 Ku kuma, ku hayayyafa, ku ruɓanɓanya, ku warwatsu a ko'ina a duniya, ku ruɓanɓanya a cikinta." 8 Sai Allah ya yi magana da Nuhu da 'ya'yansa dake tare da shi cewa, 9 Amma, "Ka saurara! Zan tabbatar da alƙawarina da ku da zuriyarku dake biye da ku, da kuma 10 dukkan halittu masu rai dake tare da ku, da tsuntsaye, da dabbobin gida, da kowacce halitta ta duniya dake tare da ku, da kuma duk abin da ya fito daga cikin jirgin, da kuma dukkan halittu masu rai dake duniya. 11 Na tabbatar da alƙawarina da ku, cewa ba zan ƙara hallakar da dukkan halittu da ruwa ba, ba za a sake yin ruwan da zai hallaka duniya ba." 12 Allah yace, "Wannan ce alamar alƙawarin da nake yi tsakanina da ku da dukkan halittun dake tare da ku, domin kuma dukkan tsararraki masu zuwa: 13 Na sa bakangizona a cikin girgije, zai kuma zama alamar alƙawarina da ku da kuma duniya. 14 Zai kuma zamana a lokacin da na sauko da girgije a kan duniya aka kuma ga bakangizo a cikin girgijen, 15 to zan tuna da alƙawarina da ku da dukkan halitta mai rai. Ruwaye ba zasu ƙara zama abin hallakarwa ga mutane ba. 16 Bakangizon zai kasance a cikin girgije, zan kuma gan shi, domin in tuna da alƙawarina madawwami, tsakanin Allah da dukkan halittu masu rai a duniya. 17 "Sai Allah yace da Nuhu, "Wannan ita ce alamar alƙawarin da na tabbatar tsakanina da dukkan masu rai na duniya." 18 'Ya'ya maza na Nuhu da suka fito daga cikin jirgin sune Shem, Ham, da kuma Yafet. Ham shi ne mahaifin Kan'ana. 19 Waɗannan guda uku sune 'ya'yan Nuhu, daga waɗannan ne aka sami dukkan mutanen duniya. 20 Nuhu ne ya fara zama manomi, ya kuma shuka garkar inabi. 21 Sai ya sha waɗansu 'ya'yan inabin, ya kuma bugu. Yana kwance a cikin rumfarsa tsirara. 22 Sai Ham mahaifin Kan'ana, ya ga tsiraicin mahaifinsa, ya kuma faɗawa 'yan'uwansa guda biyu a waje. 23 Sai Shem da Yafet suka ɗauki mayafi suka ɗora a kafaɗunsu, suka tafi da baya suka rufe tsiraicin mahaifinsu. Fuskokinsu na fuskantar wani bangon, domin haka ba su ga tsiraicin mahaifinsu ba. 24 Da Nuhu ya tashi daga mayensa, sai ya gane abin da ɗansa ƙarami ya yi masa. 25 Domin haka ya ce, "Kan'ana zai zama la'annanne. Ya zama baran barorin 'yan'uwansa." 26 Hakan nan ya ce, "Yahweh Allah na Shem, ya zama da albarka, Kan'ana kuma ya zama baransa. 27 Allah ya faɗaɗa abin mulkin Yafet, ya kuma sa gidansa a cikin rumfunan Shem. Kan'ana kuma ya zama baransa." 28 Bayan ruwan tsufana, Nuhu ya yi shekaru ɗari uku da hamsin. 29 Dukkan kwanakin Nuhu shekaru ɗari tara ne da hamsin, daga nan ya mutu.