Sura 8

1 Sai Allah ya yi la'akari da Nuhu, da dukkan dabbobin jeji, da dukkan dabbobin gida dake tare da shi a cikin jirgin ruwan. Allah ya sa iska ta hura a kan ƙasa, sai ruwaye suka fara sauka ƙasa. 2 Maɓuɓɓugai na ƙarƙas da sakatun sama aka rufe su, ruwa kuma ya ɗauke. 3 Ambaliyar ruwa kuma ta kwanta sannu a hankali daga ƙasa, bayan kuma kwanaki ɗari da hamsin, sai ruwa ya yi ƙasa. 4 Sai jirgin ruwan ya sami sauka a wata na bakwai, a ranar sha bakwai ga wannan watan, a kan duwatsun Ararat. 5 Ruwan ya ci gaba da sauka har wattanni goma. A rana ta farko ta watan, sai ƙonƙolin duwatsu suka bayyana. 6 Sai ya zamana bayan kwanaki arba'in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin ruwan da ya yi. 7 Ya aiki hankaka ya yi ta kai da komowa har sai da ruwa ya tsane daga duniya. 8 Daga nan sai ya aiki kurciya ta ga yadda ruwan ya tsane daga ƙasa, 9 amma kurciyar ba ta sami wurin sauka ba, sai ta koma gare shi cikin jirgin ruwan, domin har ya zuwa lokacin ruwa na rufe da ƙasa baki ɗaya. Sai ya miƙa hannunsa ya kamo ta ya shigar da ita cikin jirgin ruwan tare da shi. 10 Sai ya jira na tsawon ƙarin kwanaki bakwai, sa'an nan sai ya sake aiken kurciyar daga cikin jirgin ruwan. 11 Kurciyar ta koma wurinsa da yamma. Duba! a cikin bakinta ta tsinko sabon ganyen zaitun. Daga nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga ƙasa 12 Sai ya ƙara jira na waɗansu kwanaki bakwai, sai ya sake aiken kurciyar. Ba ta sake komawa wurinsa ba. 13 Sai ya zamana a shekara ta ɗari shida a farkon shekara, a wata na farko, a ranar farko ta wata, sai dukkan ruwa ya bushe daga dukkan ƙasa. Nuhu ya buɗe rufin jirgin ruwan, ya dudduba ya ga ƙasa ta bushe. 14 A cikin wata na biyu, a ranar ashirin da bakwai ga wata, ƙasa ta bushe. 15 Sai Allah yace da Nuhu, 16 "Ka fito daga cikin jirgin ruwan da kai da matarka da 'ya'yanka da matan 'ya'yanka tare da kai. 17 Ka kuma kwaso kowacce halitta mai rai dake tare da kai, da tsutsaye, da dabbobi da duk abin da ke rarrafe a doron ƙasa - domin su hayayyafa, su zama babbar runduna ta masu rai a ko'ina a duniya, su hayayyafa, su ruɓamɓanya a cikin duniya." 18 Sai Nuhu ya fita tare da 'ya'yansa, da matarsa da matan 'ya'yansa. 19 Da kowacce irin hallitta dake tare da shi da dukkan masu rarrafe da dukkan tsuntsaye da duk wani abu mai motsi bisa duniya, bisa ga irinsu, suka fito daga cikin jirgin ruwan. 20 Nuhu ya gina bagadi ga Yahweh. Ya ɗauki waɗansu daga cikin dabbobi masu tsarki da tsuntsaye masu tsarki ya miƙa hadaya ta ƙonawa da su akan bagadin. 21 Yahweh ya shaƙi ƙanshin hadayar sai ya ce a cikin zuciyarsa, "Ba zan sake la'anta ƙasa saboda mutum ba, koda yake nufe-nufen mutane a zukatansu mugunta ne tun daga yarantakarsu. Ba zan ƙara hallakar da duk masu rai ba kamar yadda na yi. 22 Muddin duniya tana nan, lokacin iri da lokacin girbi, sanyi, da zafi, bazara da damuna, dare da rana ba za su taɓa ƙarewa ba."