Sura 7

1 Yahweh yace da Nuhu, "Ka zo, da kai da dukkan gidanka, zuwa cikin jirgin, domin na ga kai mai adalci ne a gabana a wannan tsara. 2 Da dukkan dabbobi masu tsarki tare da kai, maza bakwai mata bakwai. Daga dukkan dabbobi marasa tsarki ka ɗauko biyu-biyu. 3 Hakanan daga tsuntsayen sararin sama, ka kawo maza bakwai da mata bakwai daga cikinsu, domin a tanadi irinsu a faɗin duniya. 4 Domin a rana ta bakwai zan sa a yi ruwa a dukkan duniya har kwana arba'in dare da rana. Zan hallakar da dukkan masu rai dana halitta daga fuskar duniya" 5 Nuhu ya yi dukkan abin da Yahweh ya umarce shi. 6 Nuhu yana da shekaru ɗari shida a lokacin da aka yi ruwan tsufana a duniya. 7 Da Nuhu, da 'ya'yansa maza, da matarsa, da matan 'ya'yansa maza suka shiga jirgin saboda ruwan tsufana. 8 Dabbobi masu tsarki da tsuntsaye da duk abu mai rarrafe a ƙasa, 9 biyu-biyu, namiji da mace, suka zo wurin Nuhu suka shiga akwatin, kamar yadda Allah ya umarci Nuhu. 10 Sai ya zamana bayan kwanaki bakwai, ruwan tsufana ya sauko a duniya. 11 A shekaru ɗari shida na Nuhu, a wata na biyu, a ranar sha bakwai ga wata, a dai wannan ranar, sai dukkan taskoki na zurfafa suka buɗe suka fashe, sakatun sama suka buɗe, 12 Ruwa ya fara sauka a duniya har kwanaki arba'in dare da rana. 13 A wannan ranar dai Nuhu da 'ya'yansa, Shem da Ham da Yafet da matar Nuhu, da matan 'ya'yan Nuhu uku na tare da su, suka shiga jirgin. 14 Suka shiga tare da dukkan dabbobin jeji kowanne bisa ga irinsa, da kuma kowacce irin dabba ta gida bisa ga irinta, da kuma duk abu mai rarrafe da kowaɗanne irin tsuntsaye bisa ga irinsu, da dukkan wata hallitta mai fuka-fukai. 15 Biyu daga dukkan hallitar dake da numfashin rai suka shiga jirgin tare da Nuhu. 16 Dabbobi da dukkan hallitun da suka shiga sun shiga ne kamar yadda Allah ya umarce shi. Sai Yahweh ya kulle ƙofar bayan sun shiga. 17 Sai ruwan tsufana ya sauko a duniya kwanaki arba'in, ruwan kuma ya ƙaru ya ɗaga akwatin sama da ƙasa. 18 Ruwa ya rufe duniya gaba ɗaya jirgin kuma yana ta lilo a saman ruwa. 19 Ruwa ya tumbatsa sosai a duniya har ya rufe dukkan duwatsu dake ƙarƙashin sama. 20 Ruwan ya kai har taki shida a bisa duwatsu 21 Dukkan halittu dake motsi bisa duniya suka mutu; tsuntsaye, da dabbobin gida dana daji, dukkan dabbobi dake da yawa waɗanda ke duniya da kuma dukkan mutane. 22 Da dukkan hallitun dake bisa ƙasa, waɗanda ke da numfashin rai a hancinsu, suka mutu. 23 Kowanne abu mai rai dake bisa duniya an shafe su, daga mutane ya zuwa manyan dabbobobi, da duk masu rarrafe, ya zuwa tsuntsayen sama. Dukkan su an hallakar da su daga duniya. Sai Nuhu da waɗanda ke tare da shi ne suka rage. 24 Ruwan bai janye daga ƙasa ba har kwanaki ɗari da hamsin.