Sura 49

1 Daga nan Yakubu ya kirawo 'ya'yansa maza, ya kuma ce: "Ku tattara kanku tare, domin in gaya maku abin da zai faru daku a gaba. 2 Ku tattara kanku ku kuma saurara, ku 'ya'yan Yakubu. Ku saurari Isra'ila, mahaifinku. 3 Ruben, kai ne ɗan fãrina, ƙarfina, da farkon ƙarfina, ka yi fice wajen jamali, ka kuma yi fice wajen iko. 4 Marar kamewa kamar ruwan dake ambaliya, ba zaka yi muhimmanci ba, saboda ka hau bisa gadon mahaifinka. Daga nan ka gurɓata shi; ka hau bisa gadona. 5 Simiyon da Lebi 'yan'uwa ne. Makaman ta'addanci ne takubbansu. 6 Ya raina, kada ka zo cikin shawararsu; kada ka shiga cikin taruwarsu, domin zuciyata ta fi haka daraja sosai. Domin cikin fushinsu sun kashe mutane. Saboda annashuwa ne suka turke shanu. 7 Bari fushinsu ya la'ana, domin mai zafi ne - hasalarsu kuma domin mai tsanani ce. Zan rarraba su a Yakubu in kuma warwatsa su a Isra'ila. 8 Yahuda, 'yan'uwanka zasu yabe ka. Hannunka zai kasance bisa wuyan maƙiyanka. 'Ya'yan mahaifinka za su rusuna a gabanka. 9 Yahuda ɗan zaki ne. ‌Ɗana, ka haura daga kamammunka. Ka duƙa, ka rarrafa kamar zaki, kamar zakanya. Wa zai kuskura ya tada kai? 10 Sandan sarauta ba za ta fita daga Yahuda ba, ko sandar mulki daga tsakanin ƙafafunsa, har sai Shilo ya zo. Al'ummai zasu yi masa biyayya. 11 Yana ɗaure jakinsa ga kuringar inabinsa, da ɗan jakinsa ga zaɓaɓɓiyar kuringar inabinsa, ya wanke tufafinsa cikin ruwan inabi, da alkyabbarsa cikin jinin inabi. 12 Idanunsa zasu yi duhu kamar ruwan inabi, haƙoransa kuma farare kamar madara. 13 Zebulun zai zauna a gaɓar teku. Zai zama masaukin jiragen ruwa, kuma kan iyakarsa za ta zarce har zuwa Sidon. 14 Issaka jaki ne mai ƙarfi, yana zaune a tsakiyar turakun tumaki. 15 Yana ganin wurin hutawa mai kyau da ƙasa mai gamsarwa. Zai sunkuyar da kafaɗarsa domin kaya ya kuma zama bawa domin hidimar. 16 Dan zai hukunta mutanensa a matsayin ɗaya daga cikin kabilun Isra'ila. 17 Dan zai zama maciji a gefen hanya, maciji mai dafi a tafarki dake cizon kofaton doki, saboda mahayinsa ya fãɗi ta baya. 18 Ina jiran cetonka, Yahweh. 19 Gad - mahaya zasu kai masa hari, amma zai kai masu hari ta diddigensu. 20 Abincin Asha zai zama wadatacce, zai kuma bayar da girke-girken sarauta. 21 Naftali sakakkiyar barewa ce; zai haifi kyawawan 'ya'ya. 22 Yosef mai hayayyafa ne, mai bayar da 'ya'ya ne, mai bayar da 'ya'ya dake gefen ƙorama wanda rassansa ke hawan katanga. 23 Maharba zasu kai masa hari, su kuma harbe shi, su firgita shi. 24 Amma bakansa zai tsaya dai-dai, kuma hannayensa zasu ƙware saboda hannayen Mai Iko na Yakubu, saboda sunan Makiyayi, Dutsen Isra'ila. 25 Allah na mahaifinka zai taimakeka kuma Allah Mai Iko Dukka zai albarkace ka da albarkun sararin sama, albarkun zurfafa dake kwance ƙarƙashin ƙasa, da albarkun nonna da mahaifa. 26 Albarkun mahaifinka sun fi albarkun duwatsun zamanin dã ko abubuwan marmari na tuddan dã. Bari su kasance bisa kan Yosef, har bisa rawanin dake kan yariman 'yan'uwansa. 27 Benyamin damisa ne mayunwaci. Da safe zai lanƙwame kamammensa, da yamma kuma zai raba ganimarsa." 28 Waɗannan ne kabilu sha biyu na Isra'ila. Wannan ne abin da mahaifinsu ya ce masu sa'ad da ya albarkace su. Kowannen su ya albarkace shi bisa ga albarkar da ta dace. 29 Daga nan ya umarce su ya ce masu, "Ina gaf da tafiya ga mutanena. Ku bizne ni tare da kakannina a kogon dake cikin gonar Ifron Bahittiye, 30 a cikin kogon dake cikin gonar Makfela, wadda ke kusa da Mamri a ƙasar Kan'ana, gonar da Ibrahim ya saya a matsayin maƙabarta daga hannun Ifron Bahittiye. 31 A nan ne aka bizne Ibrahim da matarsa Saratu; a nan ne suka bizne Ishaku da matarsa Rebeka; a nan ne kuma na bizne Liya. 32 Gonar da kogon dake cikin ta an saye su ne daga mutanen Het." 33 Da Yakubu ya gama waɗannan umarnai ga 'ya'yansa, ya ja ƙafafunsa cikin gadonsa, ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma tafi wurin mutanensa.