Sura 48

1 Sai ya kasance bayan waɗannan abubuwa, sai wani ya cewa Yosef, "Duba, mahaifinka bai da lafiya." Sai ya ɗauki 'ya'yansa maza biyu tare da shi, Manasse da Ifraim. 2 Sa'ad da aka gaya wa Yakubu, "Duba, ɗanka Yosef ya iso ya ganka," Isra'ila ya ƙoƙarta kuma ya zauna bakin gado. 3 Yakubu ya cewa Yosef, "Allah maɗaukaki ya bayyana a gare ni a Luz cikin ƙasar Kan'ana. 4 Ya albarkace ni ya kuma ce mani, 'Duba, zan sa ka hayayyafa, ka kuma ruɓanɓanya. Zan maida kai taron al'ummai. Zan bayar da wannan ƙasar ga zuriyarka a matsayin madawwamiyar mallaka.' 5 Yanzu 'ya'yanka biyu maza, waɗanda aka haifa maka a ƙasar Masar kafin in zo wurinka a Masar, nawa ne. Ifraim da Manasse zasu zama nawa, kamar yadda Ruben da Simiyon suke nawa. 6 'Ya'yan da zaka haifa bayan su zasu zama naka; za a lissafa su ƙarƙashin sunayen 'yan'uwansu a cikin gãdonsu. 7 Amma game da ni, sa'ad dana zo daga Faddan, cikin baƙincikina Rahila ta mutu a ƙasar Kan'ana a kan hanya, yayin da da sauran tazara a isa Ifrat. Na bizne ta a nan a kan hanyar zuwa Ifrat" (wannan ce, Betlehem). 8 Sa'ad da Isra'ila ya ga 'ya'yan Yosef maza, ya ce, "Na wane ne waɗannan?" 9 Yosef yace wa mahaifinsa, "'Ya'yana ne, waɗanda Allah ya bani a nan." Isra'ila yace, "Kawo su wurina, domin in sa masu albarka." 10 Yanzu dai idanun Isra'ila na kasawa saboda shekarunsa, har baya iya gani. Sai Yosef ya kawo su kusa da shi, kuma ya sumbace su ya kuma rungume su. 11 Isra'ila ya cewa Yosef, "Banyi tsammanin zan sa ke ganin fuskarka ba, amma Allah ya bar ni inga 'ya'yanka ma." 12 Yosef ya fito da su daga tsakanin guiwoyin Isra'ila, Daga nan kuma ya rusuna da fuskarsa ƙasa. 13 Yosef ya ɗauke su biyun, Ifraim a hannun damansa zuwa hannun hagun Isra'ila, Manasse kuma a hannun hagunsa zuwa hannun damar Isra'ila, ya kuma matso da su kusa da shi. 14 Isra'ila ya miƙa hannunsa na dama ya kuma ɗora bisa kan Ifraim, wanda shi ne ƙarami, hannun hagunsa kuma bisa kan Manasse. Ya gitta hannuwansa, domin Manasse shi ne ɗan fãri. 15 Isra'ila ya albarkaci Yosef, yana cewa, "Allah wanda a gabansa ubannina Ibrahim da Ishaku suka yi tafiya, Allah wanda ya lura da ni har ya zuwa yau, 16 mala'ikan da ya kiyaye ni daga dukkan bala'i, bari ya albarkaci waɗannan samari. Bari a raɗa sunana a sunansu, da sunan ubannina Ibrahim da Ishaku. Bari su yaɗu su yi tururu a bisa duniya." 17 Sa'ad da Yosef ya ga cewa mahaifinsa ya ɗora hannunsa na dama bisa kan Ifraim, bai ji daɗi ba. Ya ɗauke hannun mahaifinsa domin ya matsa da shi daga bisa kan Ifraim zuwa bisa kan Manasse. 18 Yosef yace wa mahaifinsa, "Ba haka ba, babana; domin wannan shi ne ɗan fãrin. Ka ɗora hannunka na dama bisa kansa." 19 Mahaifinsa ya ƙi ya kuma ce, "Na sani, ɗana, Na sani. Shi ma zai zama jama'a, shima kuma zai zama babba. Duk da haka ƙanensa zai fi shi girma, kuma zuriyarsa zasu zama al'ummai tururu." 20 Isra'ila ya albarkace su a wannan rana da waɗannan maganganu, "Mutanen Isra'ila zasu furta albarku da sunayenku suna cewa, 'Bari Allah ya maida ku kamar Ifraim kamar Manasse kuma'." Ta wannan hanya, Isra'ila ya sanya Ifraim gaba da Manasse. 21 "Isra'ila ya cewa Yosef, "Duba, ina gaf da mutuwa, amma Allah zai kasance tare da ku, zai kuma maida ku ƙasar ubanninku. 22 Game da kai, a matsayin wanda aka ɗora sama da 'yan'uwansa, Na baka gangaren tsaunin dana karɓe daga hannun Amoriyawa da takobina da kuma bakana."