Sura 47

1 Daga nan Yosef ya shiga ya gaya wa Fir'auna, "Mahaifina da 'yan'uwana, da garkunan tumakinsu da na awaki, da garkunan shanunsu, da dukkan abin da ke nasu, sun iso daga ƙasar Kan'ana. Duba, suna ƙasar Goshen." 2 Ya ɗauki biyar daga cikin 'yan'uwansa ya kuma gabatar da su ga Fir'auna. 3 Fir'auna ya cewa 'yan'uwansa, "Mene ne sana'arku?" Suka cewa Fir'auna, "Bayinka makiyaya ne, kamar kakanninmu." 4 Daga nan suka cewa Fir'auna, "Mun zo ɗan zama ne a ƙasar. Babu makiyaya domin garkunan bayinka, saboda yunwar ta yi tsanani a ƙasar Kan'ana. To yanzu, muna roƙonka bari bayinka su zauna a ƙasar Goshen." 5 Daga nan Fir'auna ya yi magana da Yosef, ya ce, "Mahaifinka da 'yan'uwanka sun zo wurinka. 6 ‌Ƙasar Masar na gabanka. Ka zaunar da mahaifinka da 'yan'uwanka a lardi mafi kyau, ƙasar Goshen. Idan ka san maza ƙwararru daga cikinsu, ka sanya su kiwon dabbobi na." 7 Daga nan Yosef ya shigo da Yakubu mahaifinsa ya kuma gabatar da shi ga Fir'auna. Yakubu ya albarkaci Fir'auna. 8 Fir'auna ya cewa Yakubu, "Tsawon rayuwarka nawa?" 9 Yakubu ya cewa Fir'auna, "Shekarun yawace-yawace na ɗari ne da talatin. Shekarun rayuwata kima ne kuma cike da wahala. Ba su kai yawan na kakannina ba." 10 Daga nan Yakubu ya albarkaci Fir'auna ya kuma fita daga gabansa. 11 Daga nan Yosef ya zaunar da mahaifinsa da 'yan'uwansa. Ya ba su gunduma a ƙasar Masar, yankin ƙasar mafi kyau, a ƙasar Ramesis, kamar yadda Fir'auna ya umarta. 12 Yosef ya wadata abinci domin mahaifinsa, da 'yan'uwansa, da dukkan gidan mahaifinsa, bisa ga lissafin masu dogara da su. 13 Yanzu dai babu abinci a dukkan ƙasar; domin yunwar ta yi tsanani. ‌Ƙasar Masar da ƙasar Kan'ana suka lalace saboda yunwar. 14 Yosef ya tattara dukkan kuɗaɗen dake ƙasar Masar da ƙasar Kan'ana, ta wurin sayar da hatsi ga mazaunan. Daga nan Yosef ya kawo kuɗaɗen fãdar Fir'auna. 15 Sa'ad da aka gama kashe dukkan kuɗaɗen dake ƙasashen Masar da Kan'ana, dukkan Masarawa suka zo wurin Yosef suka ce, "Ka bamu abinci! Ya ya zamu mutu a gabanka saboda kuɗaɗenmu sun ƙare?" 16 Yosef yace, "Idan kuɗaɗenku sun ƙare, ku kawo dabbobinku ni zan kuma baku abinci misanya domin dabbobinku." 17 Sai suka kawo dabbobinsu wurin Yosef. Yosef ya basu abinci misanya domin dawakai, domin garkunan tumaki da awaki, domin garkunan shanu, domin kuma jakuna. A wannan shekarar ya ciyar dasu da abinci a misanyar dukkan dabbobinsu. 18 Sa'ad da shekara ta ƙare, suka zo wurinsa a shekara ta gaba suka kuma ce masa, "Ba zamu ɓoye ba daga shugabanmu cewa kuɗaɗenmu sun tafi, kuma garkunan shanun na shugabanmu ne. Babu abin da ya rage a idanun shugabana, sai jikkunanmu kawai da ƙasarmu. 19 Yaya zamu mutu a gaban idanunka, dukkanmu da ƙasarmu? Ka saye mu da ƙasarmu a musanya domin abinci, mu da ƙasarmu mu zama bayi ga Fir'auna. Ka bamu iri domin mu rayu kada mu mutu, kada kuma ƙasar ta zama kufai." 20 Saboda haka Yosef ya saye wa Fir'auna dukkan ƙasar Masar. Domin kowanne Bamasare ya sayar da gonarsa, saboda yunwar ta yi tsanani sosai. Ta wannan hanya, ƙasar ta zama ta Fir'auna. 21 Game da mutanen, ya mayar dasu bayi daga ƙarshen kan iyakar Masar zuwa ɗaya ƙarshen. 22 ‌Ƙasar firistoci ce kawai Yosef bai saya ba, saboda ana ba firistocin albashi. Suna ci daga kason da Fir'auna yake ba su. Saboda haka basu sayar da gonarsu ba. 23 Daga nan Yosef ya cewa mutanen, "Duba, na saye wa Fir'auna ku da ƙasarku. Yanzu ga iri domin ku, zaku kuma noma ƙasar. 24 Da kaka tilas ku bada kaso biyar ga Fir'auna, kashi huɗu kuma zai zama naku, domin iri na gonaki domin kuma abinci domin gidajenku da 'ya'yanku." 25 Suka ce, "Ka ceci rayukanmu. Bari mu sami tagomashi a idanunka. Zamu zama bayin Fir'auna." 26 Sai Yosef ya maida haka doka mai aiki har wayau a ƙasar Masar, cewa kashi biyar na Fir'auna ne. ‌Ƙasar firistoci ce kawai ba ta zama ta Fir'auna ba. 27 Saboda haka Isra'ila ya zauna a ƙasar Masar, a ƙasar Goshen. Mutanensa suka sami mallakar wurin. Suka hayayyafa suka ruɓanɓanya sosai. 28 Yakubu ya zauna a ƙasar Masar shekaru sha bakwai, saboda haka shekarun rayuwar Yakubu ɗari da arba'in da bakwai ne. 29 Sa'ad da lokaci ya kusato da Isra'ila zai mutu, ya kira ɗansa Yosef yace masa, "Yanzu idan na sami tagomashi a idanunka, ka sanya hannunka a ƙarƙashin cinyata, ka kuma nuna mani aminci da yarda. Ina roƙon ka kada ka bizne ni a Masar. 30 Sa'ad da na yi barci da ubannina, zaka ɗauke ni ka fitar da ni daga Masar ka kuma bizne ni a maƙabartar kakannina." Yosef yace, "Zan yi yadda ka ce." 31 Isra'ila yace, "Ka rantse mani," Yosef kuma ya rantse masa. Daga nan Isra'ila ya rusuna a bisa kan gadonsa.