Sura 46

1 Isra'ila ya kama hanyarsa da dukkan abin da yake da shi, ya kuma tafi Bayersheba. A can ya miƙa hadayu ga Allah na mahaifinsa Ishaku. 2 Allah ya yi magana da Isra'ila a cikin wahayi da dare, cewa, "Yakubu, Yakubu." Ya ce, "Ga ni nan." 3 Ya ce, "Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron gangarawa zuwa Masar, domin a can zan maida kai babbar al'umma. 4 Zan gangara da kai zuwa cikin Masar, kuma tabbas zan sake hawo da kai kuma Yosef zai rufe idanunka da hannunsa." 5 Yakubu ya taso daga Bayersheba. 'Ya'yan Isra'ila suka tafi da Yakubu mahaifinsu, 'ya'yansu, da matayensu, a cikin kekunan shanun da Fir'auna ya aiko a ɗauke shi. 6 Suka ɗauki dabbobinsu da mallakarsu da suka tattara a ƙasar Kan'ana. Suka zo cikin Masar, Yakubu da dukkan zuriyarsa tare da shi. 7 Ya taho Masar tare da 'ya'yansa maza da 'ya'yan 'ya'yansa maza, da 'ya'yansa mata da 'ya'yan 'ya'yansa mata, da dukkan zuriyarsa. 8 Waɗannan ne sunayen 'ya'yan Isra'ila waɗanda suka zo Masar: Yakubu da 'ya'yansa, Ruben, ɗan fãrin Yakubu; 9 'ya'yan Ruben, Hanok, Fallu, Hezron, da Karmi; 10 'ya'yan Simiyon, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar, da Shawul, ɗan Bakan'aniya; 11 'ya'yan Lebi kuma, Gashon, Kohat, da Merari. 12 'Ya'yan Yahuda su ne Er, Onan, Shela, Ferez, da Zera, (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan'ana). 'Ya'yan Ferez su ne Hezron da Hamul. 13 'Ya'yan Issaka su ne Tola, Fuwa, Lob, da Shimron; 14 'ya'yan Zebulun sune Sered, Elon, da Yalil 15 Waɗannan ne 'ya'yan Liya waɗanda ta haifa wa Yakubu a Faddan Aram, tare da ɗiyarsa Dina. Lissafin 'ya'yansa maza da mata talatin da uku. 16 'Ya'yan Gad su ne Zefon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi, da Areli. 17 'Ya'yan Asha su ne Imna, Ishba, Ishbi, da Beriya; kuma Sera ce 'yar'uwarsu. 'Ya'yan Beriya su ne Heba da Malkiyel 18 Waɗannan ne 'ya'yan Zilfa, wadda Laban ya bayar ga ɗiyarsa Liya. Waɗannan 'ya'ya ta haifa wa Yakubu - sha shida dukka dukkansu. 19 'Ya'yan Rahila matar Yakubu su ne Yosef da Benyamin. 20 A Masar Asenat ɗiyar Fotifera firist na On, ta haifa wa Yosef Manasse da Ifraim. 21 'Ya'yan Benyamin su ne Bela, Beka, Ashbel, Gera, Na'aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim, da Ard. 22 Waɗannan ne 'ya'yan Rahila da aka haifa wa Yakubu - sha huɗu dukkan su. 23 ‌Ɗan Dan shi ne Hushim. 24 'Ya'yan Naftali su ne Yaziyel, Guni, Yeza, da Shillem. 25 Waɗannan ne 'ya'yan da Bilha ta haifa wa Yakubu, wadda Laban ya bayar ga Rahila ɗiyarsa - bakwai dukka dukkansu. 26 Dukkan waɗanda suka tafi Masar tare da Yakubu, waɗanda ke zuriyarsa, ba a ƙidaya da matayen 'ya'yan Yakubu ba, su sittin da shida ne dukkansu. 27 Tare da 'ya'yan Yosef maza biyu da aka haifa masa a Masar, yawan iyalinsa da suka tafi Masar su saba'in ne dukkansu. 28 Yakubu ya aiki Yahuda zuwa ga Yosef saboda ya nuna masa hanya a gabansa ta zuwa Goshen, suka kuma zo ƙasar Goshen. 29 Yosef ya shirya karusarsa ya kuma tafi domin ya sami Isra'ila mahaifinsa a Goshen. Ya gan shi, ya rungumi wuyansa, ya kuma yi kuka na dogon lokaci bisa wuyansa. 30 Isra'ila yace wa Yosef, "Yanzu bari in mutu, tunda na ga fuskarka, cewa kana nan da rai." 31 Yosef ya cewa 'yan'uwansa da gidan mahaifinsa, "Zan tafi in gaya wa Fir'auna, cewa, "Yan'uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke a ƙasar Kan'ana, sun zo wurina. 32 Mutanen makiyaya ne, domin suna kiwon dabbobi ne. Sun kawo garkunan tumakinsu dana awakinsu, da garkunan shanunsu, da dukkan abin da suke da shi.' 33 Zai kasance, sa'ad da Fir'auna zai kira ku ya yi tambaya, 'Mene ne sana'arku?' 34 To zaku ce masa, 'Bayinka masu kiwon dabbobi ne tun daga ƙuruciyarmu har zuwa yanzu, dukkanmu, da ubanninmu.' Ku yi haka domin ku zauna a ƙasar Goshen, domin kowanne makiyayi haramtacce ne ga Masarawa."