Sura 45

1 Daga nan Yosef bai iya kame kansa ba a gaban dukkan bayin dake tsaye a gefensa. Ya ce da ƙarfi, "Kowa ya bar ni tilas. "Babu bawan da ya tsaya a gefensa sa'ad da Yosef ya sanar da kansa ga 'yan'uwansa. 2 Ya yi kuka da ƙarfi, Masarawa suka ji, gidan Fir'auna kuma suka sami labari. 3 Yosef ya cewa 'yan'uwansa, "Ni ne Yosef. Har yanzu mahaifina nada rai?" 'Yan'uwansa ba su iya amsa masa ba, domin sun gigice a gabansa. 4 Daga nan Yosef ya cewa 'yan'uwansa, "Ku zo kusa da ni, ina roƙon ku." Suka zo kusa da shi. Ya ce, "Ni ne Yosef ɗan'uwanku, wanda kuka sayar zuwa cikin Masar. 5 Kada kuyi baƙinciki ko kuji haushin kanku saboda kun sayar da ni zuwa nan, domin Allah ya aiko ni ne gaba da ku saboda a ceci rai. 6 Domin shekaru biyu kenan yunwa na cikin ƙasar, har yanzu kuma akwai shekaru biyar inda ba za a yi huɗa ko girbi ba. 7 Allah ya aiko ni gaba da ku domin ya adana ku a matsayin ragowa a duniya, ya kuma ajiye ku da rai ta wurin babbar kuɓutarwa. 8 Saboda haka yanzu ba ku ne kuka aiko ni nan ba amma Allah ne, kuma ya maida ni uba ga Fir'auna, shugaban dukkan gidansa, kuma mai mulki a cikin dukkan ƙasar Masar. 9 Ku yi hanzari ku tafi wurin mahaifina ku ce masa, 'Wannan ne abin da ɗanka Yosef yace, "Allah ya maida ni shugaban dukkan Masar. Ka gangaro zuwa gare ni, kada ka yi jinkiri. 10 Zaka zauna a ƙasar Goshen, zaka kuma kasance kusa da ni, kai da 'ya'yanka da 'ya'yan 'ya'yanka, da garkunan tumakinka dana awaki da garkunan shanunka, da dukkan abin da kake da shi. 11 Zan biya buƙatunka a can, domin har yanzu akwai shekaru biyar na yunwa, domin kada ku kai ga talaucewa, kai, da gidanka, da dukkan abin da kake da shi."' 12 Duba, idanunku sun ga ni, da idanun ɗan'uwanku Benyamin, cewa bakina ne ya yi magana da ku. 13 Zaku gayawa mahaifina game da dukkan ɗaukakata a Masar da dukkan abin da kuka gani. Zaku yi hanzari ku kawo mahaifina a nan." 14 Ya rungume wuyan ɗan'uwansa Benyamin ya kuma yi kuka, Benyamin kuma ya yi kuka a wuyansa. 15 Ya sumbaci dukkan 'yan'uwansa kuma ya yi kuka a kansu. Bayan wannan 'yan'uwansa suka yi magana da shi. 16 Aka faɗi labarin al'amarin a gidan Fir'auna: "'Yan'uwan Yosef sun zo." Abin ya gamshi Fir'auna da bayinsa sosai. 17 Fir'auna ya cewa Yosef, "Ka cewa 'yan'uwanka, 'Ku yi haka: Ku yi wa dabbobinku kaya ku kuma tafi ƙasar Kan'ana. 18 Ku ɗauko mahaifinku da gidanku dukka ku kuma zo wurina. Zan baku nagartar ƙasar Masar, kuma zaku ci dausayin ƙasar.' 19 Yanzu an umarce ku, 'Ku yi haka, ku ɗauki kekunan shanu daga ƙasar Masar domin 'ya'yanku domin matayenku kuma. Ku kuma ɗauko mahaifinku ku zo. 20 Kada ku damu da mallakokinku, domin nagartar dukkan ƙasar Masar taku ce."' 21 'Ya'ya maza na Isra'ila suka yi haka. Yosef ya basu kekunan shanu, bisa ga dokar Fir'auna, ya kuma basu guzuri domin tafiyar. 22 Ga dukkan su ya ba kowanne mutum canjin tufafi, amma ga Benyamin ya bayar da azurfa ɗari uku da canjin tufafi biyar. 23 Ya aika wannan domin mahaifinsa: jakuna goma ɗauke da kyawawan abubuwan Masar; da matan jakuna goma ɗauke da hatsi, gurasa, da sauran kayan masarufi domin mahaifinsa domin tafiyar. 24 Sai ya sallami 'yan'uwansa suka kuma yi tafiyarsu. Ya ce masu, "Ku tabbatar cewa ba ku yi faɗa ba a kan hanya." 25 Suka tafi daga Masar suka zo ƙasar Kan'ana, ga Yakubu mahaifinsu. 26 Suka gaya masa cewa, "Yosef yana nan da rai, kuma shi ne shugaba bisa dukkan ƙasar Masar." Zuciyarsa ta yi mamaki, domin bai gaskata da abin da suka faɗa masa ba. 27 Suka gaya masa dukkan maganganun Yosef da ya faɗi masu. Sa'ad da Yakubu ya ga kekunan shanun da Yosef ya aiko su da su, ruhun Yakubu mahaifinsu ya farfaɗo. 28 Isra'ila yace, "Ya isa. Yosef ɗana yana nan da rai. Zan tafi in gan shi kafin in mutu."