Sura 44

1 Yosef ya umarci ma'aikacin gidansa, ya ce, "Ka cika buhunan mutanen da abinci, iya yadda zasu iya ɗauka, ka kuma maida wa kowannen su kuɗinsa cikin bakin buhunsa. 2 Ka sanya kofina, kofin azurfa, cikin bakin buhun ƙaramin, da kuɗinsa na hatsi." Ma'aikacin ya yi yadda Yosef ya ce. 3 Da asuba, aka kuma sallami mutanen, su da jakkunansu. 4 Sa'ad da suka fice daga birnin ba su riga sun yi nisa ba, Yosef ya cewa ma'aikacinsa, "Tashi, ka bi bayan mutanen, idan kuma ka sha kansu, ka ce masu, 'Meyasa kuka maida mugunta domin nagarta? 5 Wannan ba kofin da maigidana ke sha bane, kofin da yake amfani da shi domin sihiri? Kun yi mugunta, wannan abin da kuka yi."' 6 Ma'aikacin ya sha kansu ya kuma faɗi waɗannan maganganu a gare su. 7 Suka ce masa, "Meyasa shugabana yake faɗin waɗannan maganganu haka? Bari ya yi nesa daga bayinka da zasu aikata irin wannan. 8 Duba, kuɗaɗen da muka samu a bakin buhunanmu, mun sake kawo maka su daga ƙasar Kan'ana. Ta yaya daga nan zamu yi sãtar azurfa ko zinariya daga gidan shugabanmu? 9 Duk wanda aka same shi a wurinsa daga cikin bayinka, bari ya mutu, mu kuma zamu zama bayin shugabana." 10 Ma'aikacin yace, "Yanzu kuma bari ya kasance bisa ga maganganunku. Shi wanda aka sami kofin a wurinsa zai zama bawana, ku kuma sauran zaku fita daga zargi." 11 Daga nan kowanne mutum ya yi hanzari ya sauko da buhunsa ƙasa, kowanne mutum kuma ya buɗe buhunsa. 12 Ma'aikacin ya bincike. Ya fãra da babban ya kuma ƙarashe da ƙaramin, aka kuma sami kofin a buhun Benyamin. 13 Daga nan suka kece tufafinsu. Kowanne mutum ya ɗora kaya a jakinsa suka kuma dawo cikin birni. 14 Yahuda da 'yan'uwansa suka zo gidan Yosef. Har yanzu yana nan, suka kuma rusuna a gabansa har ƙasa. 15 Yosef yace masu, "Mene ne kuka yi haka? Ba ku san cewa mutum kamar ni ina aikata sihiri ba?" 16 Yahuda yace, "Me za mu cewa shugabana? Me za mu faɗa? Ko yaya zamu baratar da kanmu? Allah ya gãno laifin bayinka. Duba, mu bayin shugabana ne, dukkan mu da wanda aka iske kofin a hannunsa." Yosef yace, 17 "Bari yayi nesa da ni da in aikata haka. Mutumin da aka iske kofin a hannunsa, wannan taliki zai zama bawana, amma game da ku sauran, ku tafi cikin salama ga mahaifinku." 18 Daga nan Yahuda ya matso kusa da shi ya kuma ce, "Shugabana, na roƙe ka bari bawanka ya faɗi magana cikin kunnuwan shugabana, bari kuma fushinka ya yi ƙuna gãba da bawanka, domin kamar dai Fir'auna kake. 19 Shugabana ya tambayi bayinsa, cewa, 'Kuna da mahaifi ko ɗan'uwa?' 20 Muka cewa shugabana, 'Muna da mahaifi, tsohon mutum, kuma da ɗan tsufansa, ƙarami ne. Amma ɗan'uwansa ya mutu, shi kaɗai kuma ya rage ga mahaifiyarsa, kuma mahaifinsa na ƙaunarsa.' 21 Daga nan ka cewa bayinka, 'Ku kawo shi nan a gare ni domin in gan shi.' 22 Bayan haka, muka cewa shugabana, 'Yaron ba zai iya barin mahaifinsa ba. Domin idan har ya bar mahaifinsa to mahaifinsa zai mutu.' 23 Daga nan ka cewa bayinka, 'Har sai ƙaramin ɗan'uwanku ya zo tare da ku, ba zaku sake ganin fuskata ba.' 24 Daga nan ya kasance sa'ad da muka tafi wurin bawanka mahaifina, muka faɗi masa maganganun shugabana. 25 Mahaifinmu yace, 'Ku sake komawa, ku sawo mana ɗan abinci.' 26 Daga nan muka ce, 'Ba za mu iya komawa ba. Idan ƙaramin ɗan'uwanmu yana tare da mu, daga nan zamu gangara mu tafi, domin ba za mu iya ganin fuskar mutumin ba har sai ƙaramin ɗan'uwanmu yana tare da mu.' 27 Bawanka mahaifina ya ce mana, 'Kun san cewa matata ta haifa mani 'ya'ya maza biyu. 28 ‌Ɗaya daga cikin su ya fita daga gare ni kuma na ce, "Tabbas an yage shi gutsu-gutsu, ban sake ganin sa ba kuma tuni." 29 Yanzu idan kuka sake ɗauke wannan daga gare ni, kuma bala'i ya zo masa, zaku gangarar da furfurata da baƙinciki zuwa Lahira.' 30 Yanzu, saboda haka, sa'ad dana koma wurin bawanka mahaifina, kuma saurayin baya tare da mu, tun da rayuwarsa ɗaure take da rayuwar yaron, 31 zai kasance, sa'ad da ya ga yaron ba ya tare da mu, zai mutu. Bayinka zasu gangara da furfurar bawanka mahaifinmu da baƙinciki zuwa Lahira. 32 Gama bawanka ya zama wanda ya tsaya domin yaron ga mahaifina na kuma ce, 'Idan ban maido maka da shi ba, daga nan zan ɗauki laifin ga mahaifina har abada." 33 Saboda haka yanzu, ina roƙon ka bari bawanka ya tsaya a maimakon yaron a matsayin bawan shugabana, bari kuma yaron ya tafi tare da 'yan'uwansa. 34 Gama ta yaya zan tafi wurin mahaifina idan yaron ba ya tare da ni? Ina tsoron in ga mugun abin da zai zo bisa mahaifina."