Sura 43

1 Yunwa ta yi tsanani a ƙasar. 2 Sai ya kasance sa'ad da suka cinye hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce masu, "Ku sake komawa; ku sayo mana ɗan abinci." 3 Yahuda yace masa, "Mutumin ya yi mana kashedi sosai, 'Ba za ku ga fuskata ba har sai ɗan'uwanku na tare da ku.' 4 Idan ka aika ɗan'uwanmu tare da mu, to za mu gangara mu je mu sayo maka abinci. 5 Amma idan ba ka aika da shi ba, ba za mu tafi ba. Domin mutumin ya ce mana, 'Ba za ku ga fuskata ba har sai ɗan'uwanku na tare da ku."' 6 Isra'ila yace, "Meyasa kuka yi mani mummunan abu haka ta wurin gaya wa mutumin cewa kuna da wani ɗan'uwan?" 7 Suka ce, "Mutumin ya yi tambaya dalla-dalla game da mu da iyalinmu. Ya ce, 'Mahaifinku yana nan da rai? Kuna da wani ɗan'uwan? Muka amsa masa bisa ga waɗannan tambayoyi. Ta yaya zamu san cewa zai ce, 'Ku kawo ɗan'uwanku nan?"' 8 Yahuda ya cewa Isra'ila mahaifinsa, "Ka aiki saurayin tare da ni. Zamu tashi mu tafi domin mu rayu kada kuma mu mutu, dukkanmu, da kai, da kuma 'ya'yanmu dukka. 9 Ni zan tsaya domin sa. Zaka riƙe ni hakkinsa. Idan ban dawo maka da shi ba na kuma tsaida shi a gabanka ba, daga nan bari in ɗauki laifin har abada. 10 Domin idan da ba mu yi jinkiri ba, tabbas da yanzu mun dawo karo na biyu. 11 Mahaifinsu Isar'ila yace masu, "Idan haka abin yake, yanzu kuyi haka. Ku ɗauki mafi kyau daga cikin amfanin ƙasar a cikin jakkunanku. Ku tafi da su kyauta ga mutumin - su man shafawa da zuma, kayan yaji da ƙaro, tsabar 'ya'yan itace dana almond. 12 Ku ɗauki kuɗi ka shi biyu a hannunku. Kuɗaɗen da aka maido maku da aka buɗe buhunanku, ku ɗauka a cikin hannunku. Wataƙila kuskure ne. 13 Ku ɗauki ɗan'uwanku kuma. Ku tashi ku sake tafiya wurin mutumin. 14 Bari Allah maɗaukaki ya baku jinƙai a gaban mutumin, domin ya sakar maku ɗaya ɗan'uwanku da Benyamin. Idan na rasa 'ya'yana, na rasa su." 15 Mutanen suka ɗauki kyautar, a hannunsu kuma suka ɗauki kuɗi kashi biyu, tare da Benyamin. Suka tashi kuma suka tafi suka gangara zuwa Masar suka je suka tsaya kuma a gaban Yosef. 16 Sa'ad da Yosef yaga Benyamin tare da su, ya cewa ma'aikacin gidansa, "Ka kawo mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya ta, domin mutanen zasu ci tare da ni da rana." 17 Ma'aikacin ya yi yadda Yosef ya ce. Ya kawo mutanen cikin gidan Yosef. 18 Mutanen suka tsorata saboda an kawo su cikin gidan Yosef. Suka ce, "Saboda kuɗaɗen da aka maido mana cikin buhunanmu a zuwanmu na farko aka kawo mu ciki, domin ya sami zarafin gãba da mu. Zai iya ɗaure mu ya ɗauke mu a matsayin bayi, ya kuma karɓe jakkunanmu." 19 Suka kusanci ma'aikacin gidan Yosef, 20 suka kuma yi magana da shi a bakin ƙofar gidan, cewa, "Shugabana, mun zo karo na farko sayen abinci. 21 Sai ya kasance, da muka isa wurin hutawa, sai muka buɗe buhunanmu, kuma, duba, kuɗin kowanne mutum na bakin buhunsa, kuɗaɗenmu kuma nada nauyinsu dai-dai. Mun sake kawo su a hannuwanmu. 22 Mun sake kuma kawo wasu kuɗaɗen domin mu sayi abinci. Ba mu san wanda ya sanya kuɗaɗenmu cikin buhunanmu ba." 23 Ma'aikacin yace, "Salama a gareku, kada ku ji tsoro. Allahnku da Allahn mahaifinku ne ya sanya kuɗaɗenku a buhunanku. Na karɓi kuɗaɗenku." Daga nan ma'aikacin ya fito da Simiyon wurinsu. 24 Ma'aikacin ya kai mutanen cikin gidan Yosef. Ya basu ruwa, suka kuma wanke ƙafafunsu. Ya ciyar da jakkunansu. 25 Suka shirya kyaututtukan domin zuwan Yosef da rana, domin sun ji cewa zasu ci abinci a nan. 26 Sa'ad da Yosef ya zo gida, suka kawo kyaututtukan dake hannuwansu cikin gidan, suka kuma rusuna a gabansa har ƙasa. 27 Ya tambayi lafiyarsu ya kuma ce, "Mahaifinku na nan lafiya, tsohon da kuka yi maganar sa? Har yau yana nan da rai?" 28 Suka ce, "Bawanka mahaifinmu yana nan lafiya lau. Har yau yana nan da rai." Suka kwanta kuma suka rusuna har ƙasa. 29 Sa'ad da ya ɗaga idanunsa ya kalli Benyamin ɗan'uwansa, ɗan mahaifiyarsa, sai ya ce, "Wannan ne ƙaramin ɗan'uwanku da kuka yi mani maganarsa?" Daga nan ya ce, "Allah ya yi maka alheri, ɗana." 30 Yosef ya yi hanzari ya fita daga ɗakin, saboda ya motsu sosai game da ɗan'uwansa. Ya nemi wurin da zai yi kuka. Ya tafi ɗakinsa ya yi kuka a can. 31 Ya wanke fuskarsa ya kuma fito. Ya kame kansa, ya ce, "A raba abincin." 32 Bayin suka yi wa Yosef hidima shi kaɗai, suka kuma yi wa 'yan'uwan hidima su kaɗai. Masarawan suka ci tare da shi su kaɗai, saboda Masarawa ba zasu ci abinci tare da Ibraniyawa ba, domin yin haka abin ƙyama ne ga Masarawa. 33 'Yan'uwan suka zauna a gabansa, na farko bisa ga matsayin haihuwarsa, ƙaramin kuma bisa ga samartakarsa. Mutanen suka yi mamaki tare. 34 Yosef ya aika masu kaso daga abincin dake gabansa. Amma kason Benyamin ya yi sau biyar fiye dana 'yan'uwansa. Suka sha suka kuma yi murna tare da shi.