Sura 42

1 Yanzu Yakubu ya sami sani cewa akwai hatsi a Masar. Ya ce wa 'ya'yansa maza, "Meyasa kuke kallon juna?" 2 Ya ce, "Ku saurara, Na ji cewa akwai hatsi a Masar. Ku gangara can ku sawo domin mu dagacan domin mu rayu kada kuma mu mutu." 3 'Yan'uwan Yosef goma suka gangara domin su sawo hatsi daga Masar. 4 Amma Benyamin, ɗan'uwan Yosef, Yakubu bai aike shi ba tare da 'yan'uwansa, saboda ya ji tsoron cewa wani bala'i na iya afko masa. 5 'Ya'yan Isra'ila na cikin waɗanda suka zo saye, domin akwai yunwa a cikin ƙasar Kan'ana. 6 Yanzu dai Yosef shi ne gwamna a ƙasar. Shi ne ke saida wa dukkan mutanen ƙasar. 'Yan'uwan Yosef suka zo suka kuma rusuna masa da fuskokinsu ƙasa. 7 Yosef ya ga 'yan'uwansa ya kuma gãne su, amma ya ɓadda masu kamarsa ya kuma yi magana da su da zafi. Ya ce masu, "Daga ina kuka fito?" Suka ce, "Daga ƙasar Kan'ana domin mu sayi abinci." 8 Yosef ya gãne 'yan'uwansa, amma su basu gãne shi ba. 9 Daga nan Yosef ya tuna da mafarkan da ya yi game da su, ya kuma ce masu, "Ku 'yan leƙen asirin ƙasa ne! kun zo ku ga sassan ƙasar da basu da tsaro." 10 Suka ce masa, "A'a, shugabana. Bayinka sun zo sayen abinci ne. 11 Dukkan mu 'ya'yan mutum ɗaya ne. Mu mutane ne masu gaskiya. Bayinka ba 'yan leƙen asirin ƙasa ba ne." 12 Ya ce masu, "A'a, kun zo ku ga sassan ƙasar da ba su da tsaro." 13 Suka ce, "Mu bayinka 'yan'uwa sha biyu ne, 'ya'yan mutum ɗaya a cikin ƙasar Kan'ana. Duba, ƙaramin mu a yau yana tare da mahaifinmu, ɗayan ɗan'uwan kuma baya da rai." 14 Yosef yace masu, "Abin da na ce maku ke nan; ku 'yan leƙen asirin ƙasa ne. 15 Ta haka za a gwada ku. Da ran Fir'auna, ba zaku bar nan ba, sai idan ƙaramin ɗan'uwanku ya zo nan. 16 Ku aiki ɗaya daga cikin ku ya je ya zo da ɗan'uwanku. Zaku zauna a kurkuku, domin a gwada maganganunku, ko akwai gaskiya a cikin ku." 17 Ya sa dukkan su a ka kulle su har kwana uku. 18 A rana ta uku Yosef yace masu, "Ku yi haka kuma ku rayu, domin ina tsoron Allah. 19 Idan ku mutane ne masu gaskiya, bari ɗaya daga cikin 'yan'uwanku a tsare shi a kurkuku, amma ku ku tafi, ku ɗauki hatsi domin yunwar gidajenku. 20 Ku kawo mani ƙaramin ɗan'uwanku domin a tabbatar da maganganunku kuma ba za ku mutu ba." Sai suka yi haka. 21 Suka cewa juna, "Babu shakka mun yi laifi game da ɗan'uwanmu yadda muka ga ƙuncin ransa sa'ad da ya roƙe mu, amma muka ƙi sauraron sa. Saboda haka wannan ƙunci ya zo bisanmu." 22 Ruben ya amsa masu, "Ban gaya maku ba, 'Kada kuyi zunubi game da saurayin, amma baku saurare ni ba? Yanzu, duba, ana neman jininsa daga hannunmu." 23 Basu san cewa Yosef ya fahimce su ba, domin akwai mai fassara a tsakanin su. 24 Ya juya daga gare su ya yi kuka. Ya kuma dawo gare su ya yi magana da su. Ya ɗauki Simiyon daga cikin su ya ɗaure shi a gaban idanunsu. 25 Daga nan Yosef ya umarci bayinsa su cika buhunan 'yan'uwansa da hatsi, kuma su maida wa kowa kuɗinsa cikin buhunsa, su kuma basu kayan masarufi domin tafiyarsu. A ka yi haka domin su. 26 Suka ɗora wa jakunansu hatsi suka kuma yi tafiyar su daga wurin. 27 Yayin da ɗaya daga cikin su ya buɗe buhunsa domin ya ciyar da jakinsa a wurin hutawar su, ya ga kuɗinsa. Duba, suna bakin buhunsa. 28 Ya cewa 'yan'uwansa, "An maida mani kuɗina, ku dube su; suna bakin buhuna." Zukatansu suka nitse, suka kuma juya suna rawar jiki ga junansu, suna cewa, "Mene ne haka da Allah ya yi mana?" 29 Suka tafi wurin Yakubu, mahaifinsu a cikin ƙasar Kan'ana suka kuma gaya masa dukkan abin da ya faru da su. Suka ce, 30 "Mutumin, ubangijin ƙasar, ya yi magana da mu da zafi ya zaci cewa mu 'yan leƙen asirin ƙasa ne. 31 Muka ce masa, "Mu mutane ne masu gaskiya. Ba 'yan leƙen asirin ƙasa bane. 32 Mu 'yan'uwa ne sha biyu, 'ya'ya maza na mahaifinmu. ‌Ɗaya baya da rai, ƙaramin kuma yau yana tare da mahaifinmu a ƙasar Kan'ana.' 33 Mutumin, ubangijin ƙasar, ya ce mana, 'Ta haka zan sani cewa ku mutane ne masu gaskiya. Ku bar ɗaya daga cikin 'yan'uwanku tare da ni, ku ɗauki hatsi domin yunwar dake gidajenku, ku kuma yi tafiyarku. 34 Ku kawo ƙaramin ɗan'uwanku wuri na. Daga nan zan sani cewa ku ba 'yan leƙen asirin ƙasa ba ne, amma ku mutane ne masu gaskiya. Daga nan zan saki ɗan'uwanku a gare ku, kuma zaku yi sana'a a ƙasar."' 35 Sai ya kasance yayin da suka zazzage buhunansu, duba, kowanne mutum jakkar azurfarsa na cikin buhunsa. Sa'ad da su da mahaifinsu suka ga jakkunan azurfarsu, sai suka tsorata. 36 Yakubu mahaifinsu ya ce masu, "Kun salwantar mani da 'ya'yana. Yosef ba shi da rai, Simiyon kuma ya tafi, kuma zaku ɗauke Benyamin. Waɗannan abubuwa dukka gãba suke da ni." 37 Ruben ya yi magana da mahaifinsa, cewa, "Kana iya kashe 'ya'yana biyu idan ban maido maka da Benyamin ba. Ka sanya shi cikin hannuwana, kuma zan sake maido maka da shi." 38 Yakubu yace, '‌Ɗana ba zai tafi tare da ku ba. Domin ɗan'uwansa ya mutu shi kaɗai kuma ya rage. Idan wani bala'i ya zo masa a hanyar da zaku tafi, daga nan zaku kawo furfurata da baƙinciki zuwa Lahira."