Sura 41

1 Sai ya kasance bayan shekaru biyu cur Fir'auna ya yi wani mafarki. Duba, yana tsaye bakin Nilu. 2 Duba, sai ga wasu shanu bakwai sun fito daga Nilu, masu ban sha'awa da ƙiba, suna kuma kiwo a cikin iwa. 3 Duba, ga wasu shanun bakwai sun fito bayan su daga cikin Nilu, marasa ban sha'awa ramammu kuma. Suka tsaya gefen waɗancan shanun a bakin kogin. 4 Daga nan shanun marasa ban sha'awa ramammu kuma suka cinye shanun masu ban sha'awa da ƙiba. Daga nan Fir'auna ya farka. 5 Daga nan kuma ya sake yin barci ya kuma sake yin mafarki karo na biyu. Duba, kawunan hatsi bakwai sun fito bisa kara ɗaya, cikakku masu kyau kuma. 6 Gashi, kawuna bakwai, ƙanana waɗanda kuma iskar gabas ke kakkaɓewa, suka fito bayan su. 7 ‌Ƙananan kawunan suka haɗiye kawunan cikakku masu kyau kuma. Fir'auna ya farka, kuma, duba, ashe mafarki ne. 8 Sai ya kasance da safe ruhunsa ya damu. Ya aika aka kira dukkan 'yan dabo da masu hikima na Masar. Fir'auna ya gaya masu mafarkansa, amma babu wani da ya iya fassara su ga Fir'auna. 9 Daga nan shugaban masu riƙon ƙoƙon sha ya ce wa Fir'auna, "A yau ina tunani game da laifuffukana. 10 Fir'auna ya yi fushi da bayinsa, ya kuma sanya ni cikin tsaro a cikin gidan shugaban masu tsaro, shugaban masu tuya tare da ni. 11 Muka yi mafarki a cikin dare ɗaya, shi da ni. Muka yi mafarki kowanne mutum bisa ga fassarar mafarkinsa. 12 Tare da mu a can akwai wani saurayin mutum Ba'ibraniye, bawan shugaban masu tsaro. Muka faɗi masa kuma ya fassara mana mafarkanmu. Ya fassara wa kowannen mu bisa ga mafarkinsa. 13 Sai ya kasance kamar yadda ya fassara mana, haka ya faru. Fir'auna ya maido ni bisa aikina, amma ɗayan ya sarƙafe shi." 14 Daga nan Fir'auna ya aika aka kuma kirawo Yosef. Nan da nan suka fito da shi daga ramin. Ya kuma yi aski, ya canza sutura, ya kuma fito zuwa wurin Fir'auna. 15 Fir'auna ya cewa Yosef, "Na yi mafarki, amma babu mai fassara. Amma na ji labarinka, cewa idan ka ji mafarki kana iya fassara shi." 16 Yosef ya amsawa Fir'auna, cewa, "Ba ni ba ne. Allah zai amsawa Fir'auna da tagomashi." 17 Fir'auna ya yi magana da Yosef, "A cikin mafarkina, duba, ina tsaye a bakin Nilu. 18 Gashi, shanu bakwai suka fito daga cikin Nilu, masu ƙiba da ban sha'awa, suna kuma kiwo cikin iwa. 19 Gashi, wasu shanun bakwai suka fito bayan su, marasa ƙarfi, marasa ban sha'awa, ramammu kuma. A cikin dukkan ƙasar Masar ban taɓa ganin wani abin rashin ban sha'awa ba kamar su. 20 Shanun marasa ƙiba da rashin ban sha'awa suka cinye shanun na farko masu ƙiba. 21 Sa'ad da suka cinye su, ba za a ma san cewa sun cinye su ba, domin sun kasance marasa ban sha'awa kamar dã. Daga nan na farka. 22 Na duba a cikin mafarkina, kuma, duba, kawuna bakwai na hatsi suka fito bisa kara ɗaya, cikakku masu kyau. 23 Gashi kuwa, ƙarin kawuna bakwai - busassu, ƙanana, waɗanda kuma iskar gabas ke kakkaɓewa - suka fito bayansu. 24 ‌Ƙananan kawunan suka haɗiye kawunan bakwai masu kyau. Na faɗi waɗannan mafarkai ga masu dabo, amma babu wani da zai yi bayyanin su a gare ni." 25 Yosef ya cewa Fir'auna, "Mafarkan Fir'auna ɗaya ne. Abin da Allah ke gaf da aiwatar wa, ya bayyana wa Fir'auna. 26 Shanun masu kyau guda bakwai shekaru bakwai ne, kawunan hatsin bakwai kuma shekaru bakwai ne. Mafarkan iri ɗaya ne. 27 Shanun bakwai ramammu marasa ban sha'awa da suka fito bayan su shekaru bakwai ne, haka nan kuma kawunan hatsin ƙanana da iskar gabas ke kakkaɓe wa shekaru ne bakwai na yunwa. 28 Wannan batun ne na faɗawa Fir'auna. Abin da Allah ke gaf da aiwatar wa ya bayyana wa Fir'auna. 29 Duba, shekaru bakwai na yalwa zasu zo cikin dukkan ƙasar Masar. 30 Shekaru bakwai na yunwa zasu zo bayan su, za a kuma manta da dukkan yalwar da aka yi a ƙasar Masar, kuma yunwar za ta lalata ƙasar. 31 Ba za a tuna da yalwar ba a cikin ƙasar saboda yunwar da za ta biyo baya, domin za ta zama da tsanani sosai. 32 Cewa an maimaita wa Fir'auna mafarkin saboda Allah ya tabbatar da al'amarin ne, kuma Allah zai aiwatar ba da daɗewa ba. 33 Yanzu bari Fir'auna ya nemi wani mutum mai fahimta da hikima, ya kuma ɗora shi bisa ƙasar Masar. 34 Bari Fir'auna ya zaɓi shugabanni bisa ƙasar, bari kuma su ɗauki kashi biyar na dukkan amfanin Masar a cikin shekaru bakwai na yalwa. 35 Bari su tattara dukkan abincin waɗannan shekaru masu kyau dake zuwa su kuma ajiye hatsi a ƙarƙashin ikon Fir'auna, domin abincin da za a yi amfani da shi a cikin biranen. Su adana shi. 36 Abincin zai zama abin wadatar wa domin ƙasar domin kuma shekaru bakwai na yunwa da zasu kasance a ƙasar Masar. Ta wannan hanyar ƙasar ba zata lalace ba ta wurin yunwar." 37 Wannan shawara ta yi kyau a idanun Fir'auna da idanun dukkan bayinsa. 38 Fir'auna ya cewa bayinsa, "Za mu iya samun wani mutum kamar wannan, wanda Ruhun Allah ke cikinsa?" 39 Sai Fir'auna ya cewa Yosef, "Tunda Allah ya nuna maka dukkan waɗannan abubuwa, babu wani mafi fahimta da hikima kamar kai. 40 Zaka kasance bisa gidana, kuma bisa ga maganar ka za a yi mulkin dukkan mutanena. A bisa kursiyi ne kawai zan fi ka girma." 41 Fir'auna ya cewa Yosef, "Duba, na sanya ka bisa dukkan ƙasar Masar." 42 Fir'auna ya cire zoben hatiminsa daga hannunsa ya sanya a hannun Yosef. Ya yi masa sutura da suturar linin mai laushi, ya kuma sanya sarƙar zinariya a wuyansa. 43 Ya sanya shi ya tuƙa karusarsa ta biyu da ya mallaka. Mutane suka yi sowa a gabansa, "Gwiwa a durƙushe." Fir'auna ya sanya shi bisa dukkan ƙasar Masar. 44 Fir'auna ya cewa Yosef, "Ni ne Fir'auna, baya gare ka kuma, babu mutumin da zai ɗaga hannunsa ko ƙafarsa a cikin dukkan ƙasar Masar." 45 Fir'auna ya kira Yosef da suna "Zafenat-Faniya." Ya ba shi Asenat, ɗiyar Fotifera firist na On, a matsayin mata. Yosef ya fita bisa ƙasar Masar. 46 Yosef yana da shekaru talatin sa'ad da ya tsaya a gaban Fir'auna, sarkin Masar. Yosef ya fita daga gaban Fir'auna, ya kuma tafi cikin dukkan ƙasar Masar. 47 A cikin shekaru bakwai na yalwa ƙasar ta fitar da amfani a yalwace. 48 Ya tattara dukkan abinci na shekaru bakwai dake cikin ƙasar Masar ya kuma sanya abincin a cikin biranen. Ya sanya a cikin kowanne birni abincin gonakin dake kewaye da shi. 49 Yosef ya ajiye hatsi kamar rairayin teku, da yawan gaske har ya daina ƙirgawa, saboda ya zarce ƙirgawa. 50 Yosef ya haifi 'ya'ya biyu kafin zuwan shekarun yunwa, waɗanda Asenat, ɗiyar Fotifa firist na On, ta haifa masa. 51 Yosef ya kira sunan ɗan fãrinsa Manasse, domin ya ce, "Allah ya sa na manta da dukkan damuwata da dukkan gidan mahaifina." 52 Ya kira sunan ɗan na biyu Ifraim, domin ya ce, "Allah ya maida ni mai bada 'ya'ya a cikin ƙasar wahalata." 53 Shekaru bakwai na yalwa da suka kasance a ƙasar Masar suka kawo ƙarshe. 54 Aka fãra shekaru bakwai na yunwa, kamar yadda Yosef ya faɗa. Aka yi yunwa a cikin dukkan ƙasashen, amma a cikin dukkan ƙasar Masar akwai abinci. 55 Sa'ad da dukkan ƙasar Masar suka fãra yunwa, mutanen suka kira ga Fir'auna da ƙarfi domin abinci. Fir'auna ya cewa dukkan Masarawa, "Ku je wurin Yosef ku kuma yi abin da ya ce." 56 Yunwa tana bisa dukkan fuskar ƙasar. Yosef ya buɗe dukkan gidajen ajiya ya sayar wa da Masarawa. Yunwa ta yi tsanani a ƙasar Masar. 57 Dukkan duniya na zuwa Masar su sayi hatsi daga wurin Yosef, saboda yunwar ta yi tsanani a dukkan duniya.