Sura 50

1 Daga nan Yosef ya rikice, ya faɗi bisa fuskar mahaifinsa, ya kuma yi kuka a bisansa, ya kuma sumbace shi. 2 Yosef ya umarci bayinsa masu ilimin magani su nannaɗe mahaifinsa. Masu ilimin maganin suka nannaɗe Isra'ila da maganin hana ruɓewa. 3 Suka ɗauki kwana arba'in, domin wannan ne tsawon lokaci idan an naɗe gawa. Masarawa suka yi masa kuka na kwana saba'in. 4 Da kwanakin makoki suka cika, Yosef ya yi magana da gidan Fir'auna, cewa, "Idan yanzu na sami tagomashi a idanunku, ina roƙonku ku yi magana da Fir'auna, ku ce, 5 'Mahaifina yasa in yi rantsuwa, cewa, "Duba, ina gaf da mutuwa. Ka bizne ni a kabarin dana gina domin kaina a ƙasar Kan'ana. A can zaka bizne ni." Yanzu bari in haye in tafi, in kuma bizne mahaifina, daga nan kuma zan dawo."' 6 Fir'auna ya amsa, "Ka tafi ka bizne mahaifinka, kamar yadda yasa ka yi rantsuwa." 7 Yosef ya haye ya tafi bizne mahaifinsa. Dukkan 'yan majalisar Fir'auna suka tafi tare da shi - dattawan gidansa, dukkan manyan masu gari na ƙasar Masar, 8 tare da dukkan gidan Yosef da 'yan'uwansa, da gidan mahaifinsa. Amma 'ya'yansu, da garkunan tumakinsu, dana awaki, da garkunan shanunsu aka bari a ƙasar Goshen. 9 Karusai da mahaya dawaki suka tafi tare da shi. Babbar ƙungiyar mutane ce sosai. 10 Sa'ad da suka iso bakin masussukar Atad a ɗayan gefen Yodan, suka yi makoki da babban makoki da baƙinciki mai tsanani. A can Yosef ya yi makokin kwana bakwai domin mahaifinsa. 11 Sa'ad da mazauna ƙasar, Kan'aniyawa, suka ga makokin a masussukar Atad, suka ce, "Wannan taro ne na baƙinciki sosai ga Masarawa." Shi yasa ake kiran wurin da suna Abel Mizrayim, wanda ke tsallaken Yodan. 12 Daga nan 'ya'yan Yakubu suka yi masa kamar yadda ya umarta. 13 'Ya'yansa suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan'ana suka kuma bizne shi a kogon cikin gonar Makfela, kusa da Mamri. Ibrahim ya sayi kogon tare da gonar a matsayin maƙabarta. Ya saya ne daga Ifron Bahittiye. 14 Bayan da Yosef ya bizne mahaifinsa, sai ya koma cikin ƙasar Masar, shi, tare da 'yan'uwansa, da dukkan waɗanda suka raka shi bizne mahaifinsa. 15 Sa'ad da 'yan'uwan Yosef suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, suka ce, "To idan Yosef ya riƙe mu da fushi gãba da mu fa, kuma yana so ya yi mana cikakkiyar sakayya domin dukkan muguntar da muka yi masa?" 16 Sai suka umarci kasancewar Yosef, suka ce, "Mahaifinka ya bada umarni kafin ya mutu, cewa, 17 'Ku gaya wa Yosef haka, "Mu na roƙonka ka gafarta laifin 'yan'uwanka da zunubinsu sa'ad da suka yi maka mugunta."' Yanzu muna roƙonka ka gafartawa bayin Allah na mahaifinka. Yosef ya yi kuka sa'ad da suka yi masa magana. 18 'Yan'uwansa kuma suka zo suka kwanta fuska ƙasa a gabansa. Suka ce, "Duba, mu bayinka ne." 19 Amma Yosef ya amsa masu, "Kada ku ji tsoro. Ina gurbin Allah ne? 20 Game da ku, kun yi niyyar mugunta a gare ni, amma Allah ya yi niyyar alheri ne, saboda a adana rayuwar mutane da yawa, kamar yadda kuka gani a yau. 21 Saboda haka, yanzu kada ku ji tsoro. Zan tanada maku da ƙananan 'ya'yanku." Ya ta'azantar dasu ta wannan hanyar ya kuma yi maganar mutunci ga zukatansu. 22 Yosef ya zauna a Masar, tare da iyalin mahaifinsa. Ya yi rayuwa shekaru ɗari da goma. 23 Yosef ya ga 'ya'yan Ifraim har zuwa tsara ta uku. Ya kuma ga 'ya'yan Makir ɗan Manasse, waɗanda aka sanya a gwiwoyin Yosef. 24 Yosef ya cewa 'yan'uwansa, "Ina gaf da mutuwa; amma tabbas Allah zai zo gare ku, ya kuma bida ku hayewa daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya rantse zai ba Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu." 25 Daga nan Yosef ya sa mutanen Isra'ila suka rantse da alƙawari. Ya ce, "Tabbas Allah zai zo gare ku. A wannan lokacin tilas ku ɗauki ƙasusuwana daga nan." 26 Sai Yosef ya mutu, da shekaru 110. Aka nannaɗe shi da maganin hana ruɓa, kuma aka ajiye shi cikin akwati.