Sura 38

1 Sai ya kasance a wannan lokaci Yahuda ya bar 'yan'uwansa ya je ya zauna da wani Ba'addulmiye, mai suna Hira. 2 Ya haɗu da wa ta ɗiyar wani mutum Bakananiye mai suna Shuwa. Ya aure ta ya kuma kwana da ita. 3 Ta ɗauki ciki ta sami ɗa, a ka sa masa suna Er. 4 Ta sake ɗaukar ciki ta sami ɗa. Ta kira sunansa Onan. 5 Ta sake samun wani ɗan ta kira sunansa Shela. A Kezib ne wurin da ta haife shi. 6 Yahuda ya samar wa Er mata, ɗan fãrinsa. Sunanta Tama ne. 7 Er, ɗan fãrin Yahuda, mugu ne a idanun Yahweh. Yahweh ya kashe shi. 8 Yahuda ya cewa Onan, "Ka kwana da matar ɗan'uwanka. Ka yi aikin ɗan'uwan miji a gare ta, ka samar wa ɗan'uwanka ɗa." 9 Onan ya san cewa ɗan ba zai zama na shi ba. Duk lokacin da ya kwana da matar ɗan'uwansa, sai ya zubar da maniyin a ƙasa domin kada ya samar wa ɗan'uwansa ɗa. 10 Abin nan da ya yi kuwa mugunta ce a idanun Yahweh. Yahweh ya kashe shi shima. 11 Daga nan Yahuda ya cewa Tama, surukarsa, "Ki yi zaman gwauruwa a gidan mahaifinki har sai Shela, ɗana, ya girma." Gama ya ji tsoro, "Shi ma wataƙila ya mutu, kamar 'yan'uwansa." Tama ta tashi ta kuma koma da zama gidan mahaifinta. 12 Bayan lokaci mai tsawo, ɗiyar Shuwa, matar Yahuda, ta mutu. Yahuda ya ta'azantu ya kuma tafi wurin sausayar tumakinsa a Timna, shi da abokinsa Hira Ba'addulmiye. 13 Aka gaya wa Tama, "Duba, surukinki zai tafi Timna domin sausayar tumakinsa." 14 Sai ta tuɓe tufafin gwaurancinta ta rufe kanta da gyale ta kuma lulluɓe jikinta. Ta zauna a ƙofar Enayim, wadda ke kan hanyar zuwa Timna. Domin ta ga Shela ya girma, amma ba a bayar da ita ba a gare shi a matsayin mata. 15 Sa'ad da Yahuda ya ganta ya zaci cewa karuwa ce saboda ta lulluɓe fuskarta. 16 Ya je wurin ta a bakin hanya ya kuma ce, "Zo, ina roƙon ki bari in kwana da ke" - domin bai san cewa surukarsa ba ce - sai kuma ta ce, "Mezaka bani domin ka kwana da ni?" 17 Ya ce, "Zan aiko maki da 'yar akuya daga garke." Ta ce, "Zaka bani diyya har sai ka aiko da ita?" 18 Ya ce, "Wacce irin diyya zan ba ki?" Ta maida amsa, "Zoben hatiminka da ɗamararka, da sandar dake a hannunka." Ya bayar dasu a gare ta ya kuma kwana da ita, sai ta sami ciki daga gare shi. 19 Ta tashi ta yi tafiyarta. Ta tuɓe lulluɓinta ta sanya tufafin gwaurancinta. 20 Yahuda ya aika da 'yar akuyar ta hannun abokinsa Ba'addulmiye saboda ya karɓo diyyar daga hannun matar, amma bai same ta ba. 21 Sai Ba'addulmiyen ya tambayi mutanen dake wurin, "Ina karuwar asiri dake zaune a Enayim a bakin hanya?" Suka ce, "Babu wata karuwar asiri dake zaune a nan." 22 Ya dawo wurin Yahuda yace, "Ban same ta ba. Kuma, mutanen wurin sun ce, 'Babu wata karuwar asiri dake zaune a nan."' 23 Yahuda yace, "Bari ta ajiye abubuwan, domin kada mu sha kunya. Tabbas, na aika da 'yar akuyar nan, amma ba ka same ta ba." 24 Sai ya kasance bayan wajen wata uku, sai a ka gaya wa Yahuda, "Tama surukarka ta aikata karuwanci, kuma tabbas, ta sami ciki ta haka." Yahuda yace, "Ku kawo ta nan bari a ƙona ta kuma." 25 Sa'ad da aka fito da ita, sai ta aika wa surukinta da saƙo, "Ta wurin mutumin dake da waɗannan nake da ciki." Ta ce, "Ina roƙon ka da ka gano mani waɗannan na waye, zoben tambarin da ɗamarar da sandar." 26 Yahuda ya gane su ya kuma ce, "Ta fi ni adalci, tunda ban bayar da ita ba a matsayin mata ga Shela, ɗana." Bai sake kwana da ita ba kuma. 27 Sai ya kasance da lokacin haihuwarta ya kai, duba, tagwaye ne ke cikin mahaifarta. 28 Sai ya kasance a lokacin da take haihuwar ɗaya ya fito da hannunsa waje, unguwar zomar ta ɗauki jan zare ta ɗaura masa a hannu ta kuma ce, "Wannan ne ya fãra fitowa." 29 Amma daga nan sai ya maida hannunsa, kuma, duba, sai ɗan'uwansa ya fito farko. Unguwar zomar ta ce, "Ya ya ka faso waje!" Sai aka sa masa suna Ferez. 30 Daga nan ɗan'uwansa ya fito, wanda yake da jan zare a hannu, aka kuma sa masa suna Zera.