Sura 39

1 Aka kawo Yosef zuwa Masar. Fotifa, maƙaddashin Fir'auna kuma hafsan masu tsaro kuma Bamasare, ya sawo shi daga Isma'ilawa, waɗanda suka kawo shi nan. 2 Yahweh yana tare da Yosef ya kuma zama wadataccen mutum. Yana zaune cikin gidan ubangidansa Bamasare. 3 Ubangidansa ya ga cewa Yahweh na tare da shi kuma Yahweh na wadata kowanne abu da ya yi. 4 Yosef ya sami tagomashi a idanunsa. Ya bautawa Fotifa. Fotifa ya maida Yosef shugaban gidansa, da kowanne abu da ya mallaka, ya sanya ƙarƙashin lurarsa. 5 Sai ya kasance tun lokacin da ya maida shi shugaba bisa gidansa da bisa kowanne abu da ya mallaka, sai Yahweh ya albarkaci gidan Bamasaren saboda Yosef. Albarkar Yahweh tana bisa kowanne abu da Fotifa yake da shi a cikin gida da gona. 6 Fotifa ya sanya kowanne abu da yake da shi a ƙarƙashin lurar Yosef. Ba ya buƙatar ya yi tunani game da komai sai dai kawai abincin da zai ci. Shi dai Yosef kyakkyawa ne gwanin sha'awa kuma. 7 Sai ya kasance bayan wannan matar ubangidansa ta yi sha'awar Yosef. Ta ce, "Ka kwana da ni." 8 Amma ya ƙi, ya kuma ce wa matar ubangidansa, "Duba, ubangidana ba ya kulawa da abin da nake yi a cikin gidan nan, kuma ya sanya kowanne abu da yake da shi a ƙarƙashin lura ta. 9 Babu wanda ya fi ni girma a cikin gidan nan. Bai hana mani komai ba sai dai ke, saboda ke matarsa ce. Ta yaya daga nan zan yi wannan irin babbar mugunta da zunubi gãba da Allah?" 10 Ta dinga magana da Yosef rana bayan rana, amma ya ƙi ya kwana da ita ko ya kasance tare da ita. 11 Sai ya kasance wata rana, Yosef ya shiga cikin gidan domin ya yi aikinsa. Babu ko ɗaya daga cikin mutanen gidan dake cikin gidan. 12 Ta kama shi ta tufafinsa ta ce kuma, "Ka kwana da ni." Ya bar tufafinsa a hannunta, ya tsere, ya fita waje kuma. 13 Sai ya kasance, sa'ad da taga cewa ya bar tufafinsa a cikin hannunta ya kuma tsere waje, 14 sai ta kira mutanen gidanta ta ce masu, "Duba, Fotifa ya kawo Ba'ibraniye ya wulaƙanta mu. Ya shigo wurina ya kwana da ni, na kuwa yi ihu. 15 Sai ya kasance sa'ad da ya ji ina ihu, sai ya bar tufafinsa tare da ni, ya tsere, ya kuma fita waje." 16 Ta ajiye tufafinsa a kusa da ita har sai da ubangidansa ya zo gida. 17 Ta faɗi masa wannan bayyani, "Ba'ibraniyen nan bawa wanda ka kawo mana, ya shigo domin ya wulaƙanta ni. 18 Sai ya kasance sa'ad da nayi ihu, ya bar tufafinsa tare da ni ya kuma tsere waje." 19 Sai ya kasance, sa'ad da ya ji bayanin da matarsa ta faɗi masa, "Wannan ne abin da bawanka ya yi mani," sai ya fusata sosai. 20 Ubangidan Yosef ya ɗauke shi ya saka shi cikin kurkuku, wurin da a ke tsaron 'yan kurkukun sarki. Ya na nan a cikin kurkukun. 21 Amma Yahweh na tare da Yosef ya kuma nuna alƙawarin aminci a gare shi. Ya kuma ba shi tagomashi a idanun shugaban kurkukun. 22 Shugaban kurkukun ya bayar da dukkan 'yan kurkukun dake cikin kurkukun cikin hannun Yosef. Duk abin da suka yi a nan, Yosef ne ke shugabancin sa. 23 Shugaban kurkuku ba ya kulawa da kowanne abu dake cikin hannunsa, saboda Yahweh na tare da shi. Duk abin da ya yi Yahweh na wadatar da shi.