Sura 37

1 Yakubu ya zauna ƙasar da mahaifinsa ke zama, a cikin ƙasar Kan'ana. 2 Waɗannan ne al'amura game da Yakubu. Yosef, wanda ke saurayi ɗan shekaru sha bakwai, yana kiwon tumaki da awaki tare da 'yan'uwansa. Yana tare da 'ya'yan Bilha da 'ya'yan Zilfa, matan mahaifinsa. Yosef yana kawo labarai marasa daɗi game da su wurin mahaifinsu. 3 Isra'ila dai yana ƙaunar Yosef fiye da dukkan 'ya'yansa maza saboda shi ɗan tsufansa ne. Ya yi masa wata riga mai kyau. 4 'Yan'uwansa suka ga cewa mahaifinsu na ƙaunarsa fiye da dukkan 'yan'uwansa maza. Suka ƙi jininsa, kuma ba su maganar alheri da shi. 5 Yosef ya yi wani mafarki, ya kuma gaya wa 'yan'uwansa game da mafarkin. Suka ƙara ƙin jininsa. 6 Yace masu, "Ina roƙon ku da ku saurari wannan mafarkin da na yi. 7 Duba, muna ta ɗaurin dammunan hatsi a gona, gashi kuwa, sai damina ya tashi ya kuma tsaya a tsaye, sai kuma, dammunanku suka zo a kewaye suka rusuna wa damina." 8 'Yan'uwansa suka ce masa, "Lallai zaka yi sarauta a kanmu? Lallai kuwa zaka yi mulki a kanmu?" Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkansa saboda kuma maganganunsa. 9 Ya sake yin wani mafarkin ya gaya wa 'yan'uwansa. Yace, "Duba, Na yi wani mafarkin: Rana da wata da taurari sha ɗaya sun rusuna mani." 10 Ya gaya wa mahaifinsa kamar yadda ya gaya wa 'yan'uwansa, mahaifinsa kuma ya tsauta masa. Yace masa, "Wanne irin mafarki ne ka yi haka? Ko hakika mahaifiyarka da Ni da 'yan'uwanka maza za mu zo mu rusuna ƙasa a gare ka?" 11 'Yan'uwansa suka yi kishin sa, amma mahaifinsa ya ajiye al'amarin a rai. 12 'Yan'uwansa suka tafi kiwon dabbobin mahaifinsu a Shekem. 13 Isra'ila ya cewa Yosef, "Ba 'yan'uwanka na kiwon dabbobin a Shekem ba? Zo, zan kuma aike ka wurin su." Yosef yace masa, "Na shirya." 14 Yace masa, "Ka tafi yanzu, ka duba ko 'yan'uwanka na lafiya ko dabbobin kuma na lafiya, sai ka kawo mani magana." Sai Yakubu ya aike shi daga Kwarin Hebron, Yosef kuma ya tafi Shekem. 15 Wani mutum ya sami Yosef. Duba, Yosef yana ta gararanba a saura. Mutumin ya tambaye shi, "Me kake nema?" 16 Yosef yace, "Ina neman 'yan'uwana ne. Ka gaya mani, ina roƙon ka, inda suke kiwon dabbobin." 17 Mutumin yace, "Sun bar nan wurin, domin na ji suna cewa, 'Bari mu tafi Dotan."' Yosef ya bi bayan 'yan'uwansa ya kuma same su a Dotan. 18 Suka hange shi daga nesa, kafin kuma ya iso kusa da su, suka shirya makirci gãba da shi su kashe shi. 19 'Yan'uwansa suka ce wa junansu, "Duba, mai mafarkin nan yana tafe. 20 Ku zo yanzu, saboda haka, bari mu kashe shi mu kuma jefa shi cikin ɗaya daga cikin ramukan. Za mu ce, 'Naman jeji ya cinye shi.' Za mu ga abin da zai fãru da mafarkansa." 21 Ruben ya ji labari, kuma ya ceto shi daga hannunsu. Ya ce, "Kada mu ɗauki ransa." 22 Ruben yace masu, "Kada ku zubar da jini. Ku jefa shi cikin wannan ramin dake cikin jeji, amma kada ku ɗora hannu a kansa" - domin ya ceto shi daga hannunsu ya maida shi wurin mahaifinsa. 23 Sai ya kasance da Yosef ya iso wurin 'yan'uwansa, suka tuɓe masa kyakkyawar rigarsa. 24 Suka ɗauke shi suka jefa shi cikin ramin. Ramin ba komai a ciki babu ma ruwa a ciki. 25 Suka zauna, su ci abinci. Suka ɗaga idanuwansu suka duba, kuma, duba, zangon Isma'ilawa na tafe daga Giliyad, tare da raƙummansu ɗauke da kayan yaji da man ƙanshi da kayan ƙanshi. Suna tafiya zasu kai su Masar. 26 Yahuda ya cewa 'yan'uwansa, "Ina ribar da ke ciki idan muka kashe ɗan'uwanmu muka kuma rufe jininsa? 27 Ku zo, mu sayar da shi ga Isma'ilawa, kada dai mu ɗora hannunmu a kansa. Gama shi ɗan'uwanmu ne, jikinmu." 'Yan'uwansa suka saurare shi. 28 Midiyawan fatake suna wuce wa. 'Yan'uwan Yosef suka jawo shi, suka fito da shi daga rijiyar. Suka sayar da Yosef ga Isma'ilawa a kan azurfa ashirin. Isma'ilawa suka ɗauki Yosef zuwa cikin Masar. 29 Ruben ya dawo ga ramin, kuma, duba, Yosef ba shi cikin ramin. Ya yage tufafinsa. 30 Ya dawo wurin 'yan'uwansa ya ce, "Yaron ba shi a wurin! Ni kuma, ina zan tafi?" 31 Suka yanka akuya, daga nan kuma suka ɗauki rigar Yosef suka tsoma a cikin jinin. 32 Sa'an nan suka kawo ta wurin mahaifinsu suka ce, "Mun tsinci wannan. Muna roƙon ka, ka duba ko rigar ɗanka ce ko a'a." 33 Yakubu ya gane ta ya ce, "Rigar ɗana ce. Naman daji ya cinye shi. Babu shakka an yayyaga Yosef gutsu-gutsu." 34 Yakubu ya yayyage tufafinsa, ya sanya tsummokara a kwankwasonsa. Ya yi makokin ɗansa kwanaki da yawa. 35 Dukkan 'ya'yansa maza da 'ya'yansa mata suka tashi domin su ta'azantar da shi, amma ya ƙi ya ta'azantu. Ya ce, "Tabbas zan gangara zuwa Lahira cikin makoki domin ɗana." Mahaifinsa ya yi kuka domin sa. 36 Midiyawa kuwa suka saida shi a Masar ga Fotifa, wani maƙaddashin Fir'auna, hafsan masu tsaro.