Sura 36

1 Waɗannan ne zuriyar Isuwa (wanda kuma a ke kira Idom). 2 Isuwa ya ɗauki matayensa daga Kan'aniyawa. Waɗannan ne matayensa: Ada ɗiyar Elon Bahittiye; Oholibama ɗiyar Ana, jikar Zibiyon Bahibbiye; 3 da Bashemat, ɗiyar Isma'il, 'yar'uwar Nebayot. 4 Ada ta haifi Elifaz da Isuwa, Bashemat kuma ta haifi Ruwel. 5 Oholibama kuma ta haifi Yewish, Yalam da Kora. Waɗannan ne 'ya'yan Isuwa waɗanda a ka haifa masa a ƙasar Kan'ana. 6 Isuwa ya ɗauki matayensa, da 'ya'yansa maza, da 'ya'yansa mata, da mutanen dake gidansa, da dabbobinsa - dukkan dabbobinsa, da dukkan mallakarsa, wadda ya tattara a ƙasar Kan'ana, ya tafi cikin wata ƙasa nesa da ɗan'uwansa Yakubu. 7 Ya yi haka ne saboda mallakarsu ta yi yawan da ba zasu iya zama tare ba. ‌Ƙasar da suka zauna ba za ta iya ɗaukar su ba saboda yawan dabbobinsu. 8 Sai Isuwa, wanda kuma a ka sa ni da Idom, ya zauna a ƙasar tudu ta Seyir. 9 Waɗannan ne zuriyar Isuwa, kakan Idomawa a ƙasar tudu ta Seyir. 10 Waɗannan ne sunayen 'ya'ya maza na Isuwa: Elifaz ɗan Ada, matar Isuwa; Ruwel ɗan Bashemat, matar Isuwa. 11 'Ya'ya maza na Elifaz sune Teman, Omar, Zefo, Gatam, da Kenaz. 12 Timna, wata ƙwarƙwarar Elifaz, ɗan Isuwa, ta haifi Amalek. Waɗannan ne jikoki maza na Ada, matar Isuwa. 13 Waɗannan ne 'ya'ya maza na Ruwel: Nahat, Zera, Shamma, da Mizza. Waɗannan ne jikoki maza na Bashemat, matar Isuwa. 14 Waɗannan ne 'ya'ya maza na Oholibama, matar Isuwa, wadda ita ce ɗiyar Ana da jikar Zibiyon. Ta haifa wa Isuwa Yewish, Yalam, da Kora. 15 Waɗannan ne kabilu a cikin zuriyar Isuwa: Zuriyar Elifaz, ɗan fãrin Isuwa: Teman, Omar, Zefo, Kenaz, 16 Kora, Gatam, da Amalek. Waɗannan ne dangogin da suka fito daga Elifaz a ƙasar Idom. Su ne jikoki maza na Ada. 17 Waɗannan ne dangogi daga Ruwel, ɗan Isuwa: Nahat, Zera, Shamma, Mizza. Waɗannan ne dangogin da suka fito daga Ruwel a cikin ƙasar Idom. Su ne jikokin Bashemat, matar Isuwa. 18 Waɗannan ne dangogin Oholibama, matar Isuwa: Yewish, Yalam, Kora. Waɗannan ne dangogin da suka fito daga matar Isuwa Oholibama, ɗiyar Ana. 19 Waɗannan ne 'ya'ya maza na Isuwa (wanda a ka sa ni da Idom), kuma waɗannan ne hakimansu. 20 Waɗannan ne 'ya'ya maza na Seyir Bahorite, mazauna ƙasar: Lotan, Shobal, Zibiyon, Ana, 21 Dishon, Eza, da Dishan. Waɗannan ne dangogin Horitiyawa, mazauna Seyir a cikin ƙasar Idom. 22 'Ya'ya maza na Lotan su ne Hori da Heman, kuma Timna 'yar'uwar Lotan ce. 23 Waɗannan ne 'ya'ya maza na Shobal: Alban, Manahat, Ebal, Shefo, da Onam. 24 Waɗannan ne 'ya'ya maza na Zibiyon: Aiya da Ana. Wannan Ana shi ne ya gano maɓulɓular ruwa mai zafi a jeji, yayin da yake kiwon jakkan Zibiyon mahaifinsa. 25 Waɗannan ne 'ya'yan Ana: Dishon da Oholibama, ɗiyar Ana. 26 Waɗannan ne 'ya'ya maza na Dishon: Hemdan, Eshban, Itran, da Keran. 27 Waɗannan ne 'ya'ya maza na Eza: Bilhan, Za'aban, da Akan. 28 Waɗannan ne "ya'ya maza na Dishan: Uz da Aran. 29 Waɗannan ne dangogin Horitiyawa: Lotan, Shobal, Zibiyon, da Ana, 30 Dishon, Eza, Dishan: Waɗannan ne dangogin Horitiyawa, bisa ga dangoginsu da aka lissafa a ƙasar Seyir. 31 Waɗannan ne sarakunan da suka yi mulki a ƙasar Idom kafin wani sarki ya yi mulki a bisa Isra'ilawa: 32 Bela ɗan Beyor, ya yi mulki a Idom, sunan birninsa kuma Dinhaba ne. 33 Sa'ad da Bela ya mutu, daga nan Yobab ɗan Zera da Bozra, ya yi mulki a gurbinsa. 34 Sa'ad da Yobab ya mutu, Husham wanda ke daga ƙasar Temanawa, ya yi mulki a gurbinsa. 35 Sa'ad da Husham ya mutu, Hadad ɗan Bedad wanda ya ci Midiyanawa da yaƙi a ƙasar Mowab, ya yi mulki a gurbinsa. Sunan birninsa Abit ne. 36 Sa'ad da Hadad ya mutu, daga nan Samla na Masreka ya yi mulki a gurbinsa. 37 Sa'ad da Samla ya mutu, daga nan Shawul na Rehobot ta gefen kogi ya yi mulki a gurbinsa. 38 Sa'ad da Shawul ya mutu, daga nan Ba'al Hanan ɗan Akbor ya yi mulki a gurbinsa. 39 Sa'ad da Ba'al-hanan ɗan Akbo, ya mutu, daga nan Hadar ya yi mulki a gurbinsa. Sunan birninsa Fawu ne. Sunan matarsa Mehetabel, ɗiyar Matred, jikar Me Zahab. 40 Waɗannan ne sunayen shugabannin kabilu daga zuriyar Isuwa, bisa ga dangoginsu da lardunansu, bisa ga sunayensu: Timna, Alba, Yetet, 41 Oholibama, Ela, Finon, 42 Kenaz, Teman, Mibzar, 43 Magdiyel, da Iram. Waɗannan ne shugabannin dangogin Idom, bisa ga mazaunansu a cikin ƙasar da suka mallaka. Wannan ne Isuwa, mahaifin Idomawa.