Sura 35

1 Allah ya cewa Yakubu, "Ka tashi, ka nufi sama zuwa Betel, ka kuma zauna a can. Ka ginawa Allah bagadi a wurin, wanda ya bayyana a gare ka sa'ad da kake gujewa Isuwa ɗan'uwanka." 2 Daga nan Yakubu ya cewa gidansa da dukkan waɗanda ke tare da shi, "Ku fitar da bãƙin alloli dake a tsakaninku, ku tsarkake kanku, ku kuma canza suturarku. 3 Daga nan mu bar nan, mu nufi sama zuwa Betel. Zan ginawa Allah bagadi a can, wanda ya amsa mani a ranar ƙuncina, kuma ya kasance tare da ni dukkan inda na nufa." 4 Sai suka ba Yakubu dukkan bãƙin alloli da suke a hannunsu, da zobban da suke a kunnuwansu. Yakubu ya bizne su a ƙarƙashin rimi dake kusa da Shekem. 5 Yayin da suke tafiya, Allah ya sanya tsoronsu ya fãɗo a bisa biranen dake kewaye da su, domin haka waɗannan mutane ba su runtumi 'ya'yan Yakubu ba. 6 Sai Yakubu ya iso Luz (wato, Betel), wadda ke cikin ƙasar Kan'ana, shi da dukkan mutanen dake tare da shi. 7 Ya gina bagadi a nan ya kira sunan wurin El Betel, saboda a wurin ne Allah ya bayyana kansa a gare shi, sa'ad da yake gudu daga ɗan'uwansa. 8 Debora, mai kula da Rebeka, ta mutu. A ka bizne ta a gangare daga Betel ƙarƙashin itacen rimi, domin haka ana kiran wurin Allon Bakut. 9 Sa'ad da Yakubu ya zo daga Faddan Aram, Allah ya sake bayyana a gare shi ya kuma albarkace shi. 10 Allah yace masa, "Sunanka Yakubu, amma ba za a sake kiran sunanka Yakubu ba. Sunanka zai zama Isra'ila ne." Sai Allah ya kira sunansa Isra'ila. 11 Allah yace masa, "Ni ne Allah Mai Iko Dukka. Ka hayayyafa ka kuma ruɓanɓanya. ‌Ƙasa da ƙungiyar ƙasashe zasu fito daga gare ka, kuma sarakuna zasu kasance cikin zuriyarka. 12 ‌Ƙasar dana bayar ga Ibrahim da Ishaku, zan bayar a gare ka. Ga zuriyarka bayanka kuma zan bayar da ƙasar." 13 Allah ya tafi daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi. 14 Yakubu ya kafa ginshiƙi a wurin da Allah ya yi magana da shi, ginshiƙin dutse. Ya zuba baikon sha a bisansa ya kuma zuba mai a kansa. 15 Yakubu ya kira sunan wurin inda Allah ya yi magana da shi, Betel. 16 Suka kama tafiya daga Betel. Yayin da suke da 'yar tazara daga Efrat, Rahila ta fãra naƙuda. Ta yi naƙuda mai wuya. 17 Yayin da take cikin azabar naƙuda, unguwar zomar ta ce mata, "Kada ki ji tsoro, domin yanzu za ki sami wani ɗan." 18 Yayin da take mutuwa, da numfashinta na mutuwa ta raɗa masa suna Ben-Oni, amma mahaifinsa ya kira shi da suna Benyamin. 19 Rahila ta mutu a ka kuma bizne ta a kan hanyar zuwa Efrat (wato, Betlehem). 20 Yakubu ya kafa ginshiƙi bisa kabarinta. Shi ne shaidar kabarin Rahila har ya zuwa yau. 21 Isra'ila ya ci gaba da tafiya ya kafa rumfarsa a gaba da hasumiyar tsaron garke. 22 Yayin da Isra'ila ke zaune a wannan ƙasa, Ruben ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra'ila kuma ya ji labari. Yakubu dai na da 'ya'ya maza sha biyu. 23 'Ya'yansa maza daga Liya su ne Ruben, ɗan fãrin Yakubu, da Simiyon, Lebi, Yahuda, Issaka, da Zebulun. 24 'Ya'yansa maza daga Rahila su ne Yosef da Benyamin. 25 'Ya'yansa maza daga Bilha, baiwar Rahila, sune Dan da Naftali. 26 'Ya'ya maza na Zilfa, baiwar Liya, su ne Gad da Asha. Dukkan waɗannan 'ya'yan Yakubu ne waɗanda a ka haifa masa a Faddan Aram. 27 Yakubu ya zo wurin Ishaku a Mamri a Kiriyat Arba (ita ce dai Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna. 28 Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin. 29 Ishaku ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, a ka kuma tattara shi ga kakanninsa, tsohon mutum cike da kwanaki. Isuwa da Yakubu, 'ya'yansa, suka bizne shi.