Sura 33

1 Yakubu ya hango, kuma, duba, Isuwa na zuwa, tare da shi kuma mutane ɗari huɗu. Yakubu ya raba 'ya'yan tsakanin Liya, Rahila, da matayen biyu barori. 2 Daga nan ya sanya matayen barori da 'ya'yansu a gaba, a biye kuma Liya da 'ya'yanta, a biye kuma Rahila da Yosef na ƙarshen su dukka. 3 Shi da kansa kuma ya tafi gaba da su. Ya rusuna zuwa ƙasa sau bakwai, har sai da ya zo kusa da ɗan'uwansa. 4 Isuwa ya rugo ya same shi, ya rungume shi, ya rungumi wuyansa, ya sumbace shi kuma. Daga nan suka yi kuka. 5 Sa'ad da Isuwa ya hanga, sai ya ga matayen da 'ya'yan. Ya ce, "Su wane ne waɗannan mutanen tare da kai?" Yakubu yace, "'Ya'yan da Allah ta wurin alherinsa ya ba bawanka ne." 6 Daga nan bayi matan suka zo gaba tare da 'ya'yansu, suka kuma rusuna. 7 Sai Liya ita ma da 'ya'yanta suka zo gaba suka rusuna. A ƙarshe kuma Yosef da Rahila suka zo gaba suka rusuna. 8 Isuwa yace, "Mene ne kake nufi da dukkan waɗannan ƙungiyoyi da na tarar?" Yakubu yace, "Domin in sami tagomashi a gaban shugabana ne." 9 Isuwa yace, "Ina da isassu, ɗan'uwana. Ka ajiye abin da kake da shi domin kanka." 10 Yakubu yace, "A'a, ina roƙon ka, idan na sami tagomashi a idanunka, to ka karɓi kyautata daga hannuna, gama babu shakka, na ga fuskar ka, kuma kamar ganin fuskar Allah ne, kuma ka karɓe ni. 11 Ina roƙon ka ka karɓi kyautata da a ka kawo maka, saboda Allah ya aiwatar da alheri zuwa gare ni, saboda kuma ina da isassu." Haka nan Yakubu ya lallashe shi, Isuwa kuma ya karɓe su. 12 Daga nan Isuwa yace, "Mu kama hanya. Zan tafi gaba kafin kai." 13 Yakubu yace masa, "Shugabana yasan cewa yaran ƙanana ne, kuma tumakin da garken dabbobin suna renon ƙananansu. Idan a ka kora su da ƙarfi a rana ɗaya, dukkan dabbobin zasu mutu. 14 Ina roƙon ka bari shugabana ya tafi gaba da bawansa. Zan yi tafiya a hankali, bisa ga saurin dabbobin dake a gabana, bisa kuma ga saurin yaran, har sai na zo ga shugabana a Seyir." 15 Isuwa yace, "Bari in bar maka wasu daga cikin mutane na dake tare da ni." Amma Yakubu yace, "Meyasa zaka yi haka? Bari in sami tagomashi a idanun ubangijina." 16 Sai Isuwa a wannan ranar ya fara tafiya bisa hanyarsa ta komawa Seyir. 17 Yakubu ya tafi Sukkot, ya gina wa kansa gida, ya yi wa dabbobinsa kuma wurin zama. Saboda haka sunan wannan wuri ana kiransa Sukkot. 18 Sa'ad da Yakubu ya zo daga Faddan Aram, ya isa lafiya a birnin Shekem, wanda ke a cikin ƙasar Kan'ana. Ya kafa sansani kusa da birnin. 19 Daga nan ya sayi filin da ya kafa rumfarsa daga hannun 'ya'yan Hamo, mahaifin Shekem, a kan jimillar azurfa ɗari. 20 A nan ya kafa bagadi, ya kuma kira shi El Elohi Isra'ila.