Sura 32

1 Yakubu shima ya tafi hanyarsa, mala'ikun Allah suka same shi. 2 Sa'ad da Yakubu ya gan su, ya ce, "Wannan sansanin Allah ne." sai ya kira sunan wannan wuri Mahanayim. 3 Yakubu ya aiki manzanni gaba da shi zuwa ga ɗan'uwansa Isuwa a cikin ƙasar Seyir, a cikin lardin Idom. 4 Ya dokace su, cewa, "Ga abin da zaku cewa shugabana Isuwa: Ga abin da bawanka Yakubu yace: 'Ina zaune tare da Laban, na kuma yi jinkirin dawowata har zuwa yanzu. 5 Ina da shanu, da jakkai, da garkunan tumaki, da awaki, bayi maza da bayi mata. Na aiko da wannan saƙon ga shugabana, domin in sami tagomashi a idanunka."' 6 Manzannin suka dawo wurin Yakubu suka kuma ce, "Munje wurin ɗan'uwanka Isuwa. Yana zuwa ya same ka, da mutane ɗari huɗu tare da shi." 7 Daga nan Yakubu ya tsorata kuma ya ji haushi. Sai ya raba mutanen dake tare da shi ya yi sansani biyu, da garkunan tumaki, da awaki, da garkunan shanu, da raƙumma. 8 Ya ce, "Idan Isuwa ya zo ga sansani ɗaya ya kawo mana hari, daga nan sansanin da ya rage zasu kuɓuce." 9 Yakubu yace, "Allah na mahaifina Ibrahim, da Allah na mahaifina Ishaku, Yahweh, wanda ya ce mani, 'Ka koma ga ƙasarka da danginka, zan kuma wadata ka,' 10 Ban cancanci dukkan ayyukanka na alƙawarin aminci ba da dukkan yarda da ka yi domin bawanka ba. Domin da sandana kawai na ƙetare wannan Yodan, yanzu kuma na zama sansanai biyu. 11 Ina roƙonka ka cece ni daga hannun ɗan'uwana, daga hannun Isuwa, domin ina jin tsoronsa, cewa zai kawo mani hari tare da iyaye matan da 'ya'yan. 12 Amma ka ce, 'Babu shakka zan sa ka wadata. Zan maida zuriyarka kamar rairayin teku, waɗanda ba za a iya lissafawa ba domin yawansu."' 13 Yakubu ya zauna nan a wannan daren. Ya ɗauki wasu daga cikin abin da yake da su a matsayin kyauta domin Isuwa, ɗan'uwansa: 14 awaki ɗari biyu da bunsuru ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin, 15 raƙuma talatin masu shayarwa da 'ya'yansu, shanu arba'in, bijimai goma, jakkai mata ashirin da jakkai maza goma. 16 Waɗannan ya bayar dasu cikin hannun bayinsa, kowanne garke daban. Ya cewa bayinsa, "Ku tafi gaba da ni, ku sanya tazara tsakanin kowanne garken." 17 Ya umarci bawa na farko, cewa, "Idan Isuwa ɗan'uwana ya gamu da kai ya tambaye ka, cewa, 'Kai na wane ne? Ina za ka je? Dabbobin wane ne waɗannan da ke gabanka?' 18 Daga nan za ka ce, 'Na bawanka ne Yakubu. Kyauta ce a ka aiko wa shugabana Isuwa. Duba, shi ma yana zuwa bayanmu."' 19 Yakubu ya sake bada umarnai ga ƙungiya ta biyu, ta uku, da dukkan mutanen da suka bi garkunan. Ya ce, "Zaku faɗi abu iri ɗaya ga Isuwa idan kuka same shi. 20 Tilas kuma ku ce, 'Bawanka Yakubu yana zuwa bayanmu."' Gama ya yi tunani, "Zan tausar da shi da kyaututtukan da nake aikawa da su a gabana. Sai daga baya, sa'ad da zan gan shi, wataƙila zai karɓe ni." 21 Sai kyaututtukan suka tafi gaba da shi. Shi kuwa da kansa ya tsaya a wannan daren a cikin sansani. 22 Yakubu ya tashi da daddare, ya kuma ɗauki matayensa biyu, da matayensa barori su biyu, da 'ya'yansa maza sha ɗaya. Ya aika da su ƙetaren kududdufin Yabbok. 23 Ta wannan hanyar ya aika da su ƙetaren rafin tare da dukkan mallakarsa. 24 A ka bar Yakubu shi kaɗai, wani mutum kuwa ya yi kokowa da shi har wayewar gari. 25 Sa'ad da mutumin ya ga cewa ba zai kayar da shi ba, sai ya mazge shi a kwankwaso. Sai kwankwason Yakubu ya goce sa'ad da yake kokowa da shi. 26 Mutumin yace, "Bari in tafi, domin gari yana wayewa." Yakubu yace, "Ba zan bar ka ka tafi ba sai ka albarkace ni." 27 Mutumin yace masa, "Yayã sunanka?" Yakubu yace, "Yakubu." 28 Mutumin yace, "Ba za a sake kiran sunanka Yakubu ba, amma Isra'ila. Gama ka yi gwagwarmaya tare da Allah tare da mutane ka kuma yi nasara." 29 Yakubu yace masa, "Ina roƙon ka, ka faɗi mani sunanka." Ya ce, "Meyasa kake tambayar sunana?" Daga nan ya albarkace shi a wurin. 30 Yakubu ya kira sunan wurin Feniyel, gama ya ce, "Na ga Allah fuska da fuska, kuma rayuwata ta kuɓuta." 31 Rana ta taso bisa Yakubu sa'ad da yake wuce Feniyel. Yana ɗangyashi saboda kwankwasonsa. 32 Shi ya sanya har wa yau mutanen Isra'ila ba su cin jijiyoyin kwankwaso waɗanda suke mahaɗin kwankwaso, saboda mutumin ya yi wa jijiyoyin rauni sa'ad da ya sa kwankwason Yakubu ya goce.