Sura 31

1 Yanzu Yakubu ya ji maganganun 'ya'yan Laban maza, cewa sun ce, "Yakubu ya ɗauke dukkan abin dake na mahaifinmu, kuma daga mallakar mahaifinmu ne ya samo dukkan wannan dukiyar." 2 Yakubu ya kalli yanayin fuskar Laban. Ya ga cewa halinsa zuwa gare shi ya canza. 3 Daga nan Yahweh ya cewa Yakubu, "Ka koma ƙasar ubanninka da danginka, zan kuma kasance tare da kai." 4 Yakubu ya aika a ka kira Rahila da Liya zuwa saura a garkensa 5 ya kuma ce masu, "Na ga halin mahaifinku zuwa gare ni ya canza, amma Allah na mahaifina yana tare da ni. 6 Kun san cewa da dukkan karfina ne na bautawa mahaifinku. 7 Mahaifinku ya ruɗe ni ya canza ladana sau goma, amma Allah bai ba shi damar cutar da ni ba. 8 Idan ya ce, "Dabbobin kyalloli zasu zama ladanka,' daga nan dukkan garken suka haifi jarirai kyalloli. Idan ya ce, "Ma su zãne zasu zama ladanka,' daga nan dukkan garken suka haifi 'ya'ya masu zãne. 9 Ta wannan hanya Allah ya ɗauke dabbobin mahaifinku ya kuma bayar da su a gare ni. 10 Sau ɗaya a lokacin yin barbara, na gani a mafarki cewa bunsuran na barbara da dabbobin. Bunsuran masu zãne ne, da kyalloli, da masu ɗigo. 11 Mala'ikan Allah yace da ni a cikin mafarkin, 'Yakubu.' Na ce, 'Ga ni nan.' 12 Ya ce, 'Ka ɗaga idanunka ka ga dukkan bunsuran dake barbara da dabbobin. Masu zãne ne, da kyalloli, da masu ɗigo, gama na ga dukkan abin da Laban yake yi maka. 13 Ni ne Allah na Betel, in da ka yi wa ginshiƙi shafewa, in da ka ɗaukar mani wa'adi. Yanzu ka tashi ka bar wannan ƙasar ka kuma koma ƙasar haihuwarka."' 14 Rahila da Liya suka amsa suka ce masa, "Akwai kuma wani rabo ko gãdo dominmu a gidan mahaifinmu? 15 Ba kamar bãre ya maida mu ba? Gama ya sayar da mu kuma ya lanƙwame kuɗinmu gabaɗaya. 16 Domin dukkan arzikin da Allah ya ɗauke daga wurin mahaifinmu yanzu na mu ne da 'ya'yanmu. To yanzu duk abin da Allah yace maka, sai ka yi." 17 Daga nan Yakubu ya tashi ya ɗora 'ya'yansa da matayensa bisa raƙumma. 18 Ya kora dukkan dabbobinsa gaba da shi, tare da dukkan kaddarorinsa, har da dabbobin da ya samu a Faddan Aram. Daga nan ya kama tafiya zuwa wurin mahaifinsa Ishaku a cikin ƙasar Kan'ana. 19 Sa'ad da Laban ya tafi yi wa tumakinsa sausaya, Rahila ta ɗauke allolin gidan mahaifinta. 20 Yakubu shi ma ya ruɗi Laban Ba'aramiye, ta wurin ƙin gaya masa cewa zai tashi. 21 Sai ya tsere da dukkan abin da yake da shi, nan da nan kuma ya wuce ƙetaren Kogi, ya kuma doshi zuwa ƙasar tudu ta Giliyad. 22 A rana ta uku a ka gaya wa Laban cewa Yakubu ya gudu. 23 Sai ya ɗauki danginsa ya kuma bi shi na tsawon tafiyar kwana bakwai. Ya sha kansa a ƙasar tudu ta Giliyad. 24 Sai Allah ya zo wurin Laban Ba'aramiye a cikin mafarki da dare ya kuma ce masa, "Ka yi hankali kada kayi magana da Yakubu mai kyau ko marar kyau." 25 Laban ya sha kan Yakubu. Yanzu Yakubu ya kafa rumfarsa a ƙasar tudu. Laban shi ma ya kafa sansani tare da danginsa a ƙasar tudu ta Giliyad. 26 Laban ya cewa Yakubu, "Mene ne ka yi, da ka ruɗe ni ka kuma ɗauke 'ya'yana mata kamar kamammun yaƙi? 27 Meyasa ka tsere a asirce ka kuma yi mani dabara ba ka kuma gaya mani ba? Da na sallame ka da biki da waƙe-waƙe, tare da tambari da garayu. 28 Ba ka bar ni na yi sumbar sallama ga jikokina da 'ya'yana ba. Yanzu ka aikata wawanci. 29 A cikin ikona ne in cutar da kai, amma Allah na mahaifinka ya yi magana da ni a daren da ya wuce ya ce, 'Ka yi hankali kada ka yi magana da Yakubu mai kyau ko marar kyau.' 30 Yanzu ka gudu saboda kana marmarin ka koma gidan mahaifinka. Amma me ya sa ka sace allolina?" 31 Yakubu ya amsa kuma ya ce wa Laban, "Saboda na ji tsoro kuma na yi tunanin za ka karɓe 'ya'yanka mata da ƙarfi daga gare ni sai na gudu a asirce. 32 Duk wanda ya sace allolinka ba zai ci gaba da rayuwa ba. A gaban dangoginmu, ka tantance abin da ke naka tare da ni ka ɗauka." Gama Yakubu bai san cewa Rahila ta sace su ba. 33 Laban ya shiga cikin rumfar Yakubu, cikin rumfar Liya, da cikin rumfar bayi matan biyu, amma bai gan su ba. Ya fita daga rumfar Liya ya shiga cikin rumfar Rahila. 34 A she Rahila ta ɗauki allolin gidan, ta sanya su a sirdin raƙumi, ta kuma zauna a bisansu. Laban ya bincike rumfar gabaɗaya, amma bai same su ba. 35 Ta ce wa mahaifinta, "Kada ka ji haushi, shugabana, cewa ba zan iya tashi ba a gabanka, domin ina cikin al'adata." Sai ya bincike amma bai ga allolin gidansa ba. 36 Yakubu ya husata ya yi gardama da Laban. Ya ce masa, "Mene ne laifi na? Mene ne zunubi na, da ka runtumo ni da zafi? 37 Gama ka duba dukkan mallakata. Me ka samu daga dukkan kayayyakin gidanka? Ka fito da su yanzu a gaban dangoginmu, sai su shar'anta a tsakanin mu biyu. 38 Shekaru ashirin ina tare da kai. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuma ci wani rago ba daga garkunanka. 39 Abin da bisashe suka yayyage ban kawo maka ba. Maimako, na ɗauki asararsa. Ko yaushe kana sa in biya duk wata dabbar da ta bace, ko wadda a ka sace da rana ko wadda a ka sace da dare. 40 Nan ni ke; da rana zafi na cinye ni, da dare cikin sanyin dusar ƙanƙara; na yi tafiya kuma babu barci. 41 Waɗannan shekaru ashirin ina cikin gidanka. Na yi maka aiki shekaru sha huɗu domin 'ya'yanka biyu mata, shekaru shida kuma domin dabbobinka. Ka canza ladana sau goma. 42 Idan ba domin Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim, da wanda Ishaku ke tsoro, yana tare da ni ba, tabbas da yanzu ka kore ni hannu wofi. Allah ya dubi tsanantawata da aiki tuƙuru dana yi, ya kuma tsauta ma ka a daren jiya." 43 Laban ya amsa ya ce wa Yakubu, "'Ya'yan mata 'ya'yana ne, jikokin jikokina ne, dabbobin kuma dabbobina ne. Dukkan abin da kake gani nawa ne. Amma me zan iya yi a yau game da waɗannan 'ya'ya matan nawa, ko kuma game da 'ya'yansu da suka haifa? 44 To yanzu, bari mu ɗauki alƙawari, kai da ni, bari kuma ya zama domin shaida tsakanin kai da ni." 45 Sai Yakubu ya ɗauki dutse ya kuma dasa shi a matsayin ginshiƙi. 46 Yakubu ya cewa danginsa, "Ku tattara duwatsu." Sai suka ɗebo duwatsu suka tattara su. 47 Laban ya kira shi Yagar Saha Duta, amma Yakubu ya kira shi Galid. 48 Laban yace, "Wannan tarin shaida ne tsakani na da kai a yau." saboda haka a ka kira sunansa Galid. 49 A na kuma kiransa Mizfa, saboda Laban yace, "Bari Yahweh ya duba tsakanin ka da ni, yayin da muka ɓace daga juna. 50 Idan ka wulaƙanta 'ya'yana mata, ko kuma ka auri wasu matan baya ga 'ya'ya na, ko da yake babu wanda ke tare da mu, duba, Allah ne shaida tsakanin ka da ni." 51 Laban ya cewa Yakubu, "Dubi wannan tarin, ka kuma dubi ginshiƙin, wanda na kafa tsakanin ka da ni. 52 Wannan tarin shaida ne, ginshiƙin kuma shaida ne, cewa ba zan ƙetare gaba da wannan tarin ba zuwa gare ka, kai kuma ba zaka ƙetare gaba da wannan tarin ba da wannan ginshiƙin zuwa gare ni ba, domin cutarwa. 53 Bari Allah na Ibrahim, da allahn Naho, da allolin mahaifinsu, su shar'anta tsakaninmu." Yakubu ya rantse da tsoron mahaifinsa Ishaku. 54 Yakubu ya miƙa hadaya a bisa tsaunin ya kuma kira danginsa su ci abinci. Suka ci suka zauna tsawon dare a tsaunin. 55 Tun da sassafe Laban ya tashi, ya sumbaci jikokinsa da 'ya'yansa mata ya albarkace su. Daga nan Laban ya tafi ya koma gida.