Sura 30

1 Da Rahila ta ga cewa ba ta haifa wa Yakubu 'ya'ya ba, sai Rahila ta ji kishin 'yar'uwarta. Ta ce wa Yakubu, "Ba ni 'ya'ya, ko in mutu." 2 Fushin Yakubu ya yi ƙuna gãba da Rahila. Ya ce, "Ina a madadin Allah ne, wanda ya hana ki samun 'ya'ya?" 3 Ta ce, "Duba, wannan baiwata ce Bilha. Ka kwana da ita, saboda ta haifi 'ya'ya bisa gwiwoyina, kuma in sami 'ya'ya ta wurin ta." 4 Sai ta bayar da baiwarta Bilha a matsayin mata, Yakubu kuma ya kwana da ita. 5 Bilha ta ɗauki ciki ta haifa wa Yakubu ɗa. 6 Daga nan Rahila ta ce, "Allah ya baratar da ni, ya kuma ji muryata ya kuma bani ɗa." Domin wannan dalili ta kira sunansa Dan. 7 Bilha, baiwar Rahila, ta sake ɗaukar ciki ta haifa wa Yakubu ɗa na biyu. 8 Rahila ta ce, "Da kokowa mai girma na yi kokowa da 'yar'uwata na kuma yi nasara." Ta kira sunansa Naftali. 9 Sa'ad da Liya ta ga cewa ta tsaya da haihuwar 'ya'ya, ta ɗauki Zilfa, baiwarta, ta bayar da ita ga Yakubu a matsayin mata. 10 Zilfa, baiwar Liya, ta haifa wa Yakubu ɗa. 11 Liya ta ce, "Wannan rabo ne!" Sai ta kira sunansa Gad. 12 Daga nan Zilfa, baiwar Liya, ta haifa wa Yakubu ɗa na biyu. 13 Liya ta ce, "Na yi murna! domin 'ya'ya mata zasu kira ni murna." Sai ta kira sunansa Asha. 14 Ruben ya fita a lokacin yankan alkama ya kuma samo 'ya'yan itacen manta'uwa daga saura. Ya kuma kawo su wurin mahaifiyarsa Liya. Daga nan Rahila ta ce wa Liya, "Ki ba ni daga cikin 'ya'yan itacen manta'uwa na ɗanki." 15 Liya ta ce mata, "‌Ƙaramin al'amari ne a gare ki, cewa kin ɗauke mani miji? Ki na so yanzu ki ɗauke 'ya'yan manta'uwa na ɗana, kuma?" Rahila ta ce, "To zai kwana dake a daren nan, a matsayin musanya domin 'ya'yan manta uwa na ɗanki." 16 Yakubu ya dawo daga gona da yamma. Liya ta fita ta same shi ta ce, "Tilas ka kwana da ni a daren nan, domin nayi hayar ka da 'ya'yan manta'uwa na ɗana." Sai Yakubu ya kwana da Liya a wannan daren. 17 Allah ya saurari Liya, ta kuma ɗauki ciki ta haifa wa Yakubu ɗa na biyar. 18 Liya ta ce, "Allah ya bani ladana, saboda na bayar da baiwata ga mijina." Sai ta kira sunansa Issaka. 19 Liya ta sake ɗaukan ciki ta haifa wa Yakubu ɗa na shida. 20 Liya ta ce, "Allah ya bani kyauta mai kyau. Yanzu mijina zai girmama ni, saboda na haifa masa 'ya'ya maza shida." Ta kira sunansa Zebulun. 21 Daga baya ta haifi ɗiya ta kuma kira sunanta Dina. 22 Allah ya tuna da Rahila ya kuma saurare ta. Ya sa ta ɗauki ciki. 23 Ta ɗauki ciki ta haifi ɗa. Ta ce, "Allah ya ɗauke kunyata." 24 Ta kira sunansa Yosef, cewa, "Yahweh ya ƙara mani wani ɗan." 25 Bayan da Rahila ta haifi Yosef, sai Yakubu yace wa Laban, "Ka sallame ni saboda in tafi nawa gidan da ƙasata. 26 Ka bani matayena da 'ya'yana waɗanda domin su na yi maka bauta, bari kuma in tafi, gama ka san hidimar dana yi maka." 27 Laban yace masa, "Idan yanzu na sami tagomashi a gaban ka, ka jira, saboda ta wurin amfani da sihiri na gane cewa Yahweh ya albarkace ni saboda kai." 28 Daga nan ya ce, "Ka faɗi ladanka, zan kuma biya su." 29 Yakubu yace masa, "Ka san dai yadda na bauta maka, da yadda dabbobinka suka kasance tare da ni. 30 Domin 'yan kaɗan kake da su kafin in zo, kuma sun ƙaru a yalwace. Yahweh ya albarkace ka a duk inda na yi aiki. Yanzu yaushe zan samar wa nawa gidan shi ma?" 31 Sai Laban yace, "Me zan biya ka?" Yakubu yace, "Ba zaka bani komai ba. Idan zaka yi wannan domina, zan sake ciyar da dabbobinka in kiwata su kuma. 32 Bari in ratsa cikin dukkan dabbobinka a yau, zan ware daga cikin su duk wasu tumaki dabbare-dabbare da masu ɗigo, da waɗanda ke baƙaƙe daga cikin tumakin, da masu ɗigo da kyalloli daga cikin awakin. Waɗannan ne zasu zama ladana. 33 Amincina zai yi shaida game da ni daga bisani, sa'ad da zaka zo ka duba ladana. Duk wadda ba kyalla ba ce ko mai ɗigo daga cikin awaki, da baƙa daga cikin tumaki, duk wadda a ka samu a wurina, a ɗauke shi a matsayin sata." 34 Laban yace, "Na yarda. Bari ya kasance bisa ga maganarka." 35 A wannan rana Laban ya ware dukkan bunsurai masu zãne da masu ɗigo, da dukkan awaki kyalloli da masu ɗigo, duk wata mai fari a jikinta, da dukkan baƙaƙe daga cikin tumaki, ya kuma bayar da su cikin hannun 'ya'yansa. 36 Laban kuma ya sa tafiya ta kwana uku tsakaninsa da Yakubu. Sai Yakubu ya ci gaba da kiwon sauran dabbobin Laban. 37 Sai Yakubu ya ɗauko ɗanyun tsabgun auduga, da rassan itacen almond da rassan itacen durumi, ya kuma fera fararen zãne a kan su, ya sanya fararen itatuwan dake cikin ƙiraren su bayyana. 38 Daga nan ya jera ƙiraren da ya feffere a gaban dabbobin, a gaban kwamamen ruwa in da suke zuwa su sha. Suna ɗaukar ciki sa'ad da suka zo shan ruwa. 39 Dabbobin suka yi ta barbara a gaban ƙiraren; dabbobin kuma suka yi ta haihuwar 'ya'yai masu zãne, da kyalloli, da masu ɗigo. 40 Yakubu ya ware waɗannan 'yan raguna, amma ya sanya sauran su fuskanci dabbobin masu zãne da dukkan baƙaƙen tumaki a garken Laban. Daga nan sai ya ware nasa dabbobin domin kansa kaɗai ba ya kuma haɗa su tare da dabbobin Laban ba. 41 A duk sa'ad da ƙarfafan tumakin ke barbara, sai Yakubu ya shimfiɗa ƙiraren nan a cikin kwamamen ruwan nan a gaban idanun dabbobin, saboda su ɗauki ciki a tsakiyar ƙiraren. 42 Amma idan dabbobi marasa ƙarfi daga cikin garken suka zo, ba ya sanya ƙiraren a gabansu. Sai ya zama dabbobin marasa ƙarfi na Laban ne, ƙarfafan kuma na Yakubu ne. 43 Mutumin ya zama wadatacce sosai. Yana da manyan garkuna, bayi mata da bayi maza, da raƙuma da jakuna.