Sura 29

1 Daga nan Yakubu ya kama tafiyarsa ya zo cikin ƙasar mutanen gabas. 2 Yayin da ya duba, sai ya ga rijiya a saura, kuma, duba, garkunan tumaki uku na kwance a gefen ta. Domin daga wannan rijiyar za su yi wa garkunan ban ruwa, kuma dutsen dake bakin rijiyar ƙato ne. 3 Sa'ad da dukkan garkunan suka taru a nan, makiyayan zasu gangarar da dutsen daga bakin rijiyar su kuma yi wa tumakin ban ruwa, sai kuma su mai da dutsen bakin rijiyar, daidai wurinsa. 4 Yakubu yace masu, "Yan'uwana, daga ina ku ke?" Suka maida amsa, "Daga Haran muke." 5 Ya ce masu, "Kun san Laban ɗan Nahor?" Suka ce, "Mun san shi." 6 Ya ce masu, "Yana nan lafiya?" Suka ce, "Yana nan lafiya, kuma, duba can, Rahila ɗiyarsa na zuwa tare da tumaki." 7 Yakubu yace, "Duba, yanzu rana tsaka ne. Lokaci bai yi ba da za a tattara garkuna tare. Kuyi wa tumakin ban ruwa daga nan ku tafi ku kai su kiwo." 8 Suka ce, "Ba za mu iya yi masu banruwa ba har sai dukkan garkunan sun tattaru tare. Daga nan mazan zasu gangarar da dutsen daga bakin rijiyar, sai kuma mu yi wa tumakin banruwa." 9 Yayin da Yakubu ke magana tare da su, Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, domin ita ke kiwon su. 10 Sa'ad da Yakubu ya ga Rahila, ɗiyar Laban, ɗan'uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, ɗan'uwan mahaifiyarsa, Yakubu ya zo kusa, ya gangarar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma yi wa garken Laban ɗan'uwan mahaifiyarsa banruwa. 11 Yakubu ya sumbaci Rahila ya yi kuka da ƙarfi. 12 Yakubu ya gaya wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne, kuma cewa shi ɗan Rebeka ne. Daga nan ta ruga ta gaya wa mahaifinta. 13 Sa'ad da Laban ya ji labarin Yakubu ɗan 'yar'uwarsa, ya ruga domin ya same shi, ya rungume shi, ya sumbace shi, ya kuma kawo shi cikin gidansa. Yakubu ya gaya wa Laban dukkan waɗannan abubuwa. 14 Laban yace masa, "Tabbas kai ƙashina ne da namana." Daga nan Yakubu ya zauna tare da shi har wajen wata ɗaya. 15 Daga nan Laban ya cewa Yakubu, "Kã bauta mani a banza saboda kai ɗan dangina ne? Gaya mani, mene ne zai zama ladanka?" 16 Yanzu dai Laban na da 'ya'ya mata biyu. Sunan babbar Liya, sunan ƙaramar kuma Rahila. 17 Idanun Liya tausasa ne amma Rahila na da kyakkyawar siffa. 18 Yakubu ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, "Zan bauta maka shekaru bakwai domin Rahila, ƙaramar ɗiyarka." 19 Laban yace, "Gwamma in bayar da ita a gare ka, maimakon in bayar da ita ga wani mutumin. Ka yi zamanka da ni." 20 Sai Yakubu ya yi bauta shekaru bakwai domin Rahila; sai kuma suka yi masa kamar kwanaki kaɗan, domin ƙaunar da yake yi mata. 21 Daga nan Yakubu ya cewa Laban, "Ka bani matata, domin kwanakina sun kammalu - domin in aure ta!" 22 Sai Laban ya tattara dukkan mutanen wurin ya kuma yi biki. 23 Da maraice ya yi, Laban ya ɗauki ɗiyarsa Liya ya kuma kawo wa Yakubu, wanda ya kwana da ita. 24 Laban ya ɗauki baiwarsa Zilfa ya ba ɗiyarsa Liya, ta zama baiwarta. 25 Da safe, da ya duba, sai ya ga ashe Liya ce! Yakubu ya cewa Laban, "Mene ne wannan ka yi mani? Ba domin Rahila na bauta maka ba? To me ya sa ka yaudare ni?" 26 Laban yace, "Ba al'adarmu ba ce mu bayar da ƙaramar ɗiya kafin ta fãrin. 27 Ka kammala satin amarcin wannan ɗiyar, za mu kuma baka ɗayar a sakamakon sake bauta mani na wasu shekarun bakwai." 28 Yakubu ya yi haka, ya kammala satin Liya. Daga nan Laban ya ba shi Rahila ɗiyarsa a matsayin matarsa. 29 Laban kuma ya bayar da Bilha ga ɗiyarsa Rahila, ta zama baiwarta. 30 Haka kuma Yakubu ya kwana da Rahila, amma ya ƙaunaci Rahila fiye da Liya. Sai Yakubu ya bauta wa Laban na wasu shekaru bakwai. 31 Yahweh ya ga cewa ba a ƙaunar Liya, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ba ta da ɗa. 32 Liya ta ɗauki ciki ta haifi ɗa, ta kuma kira sunansa Ruben. Domin ta ce, "Saboda Yahweh ya dubi azabata; babu shakka yanzu mijina zai ƙaunace ni." 33 Daga nan ta sake ɗaukan ciki ta haifi ɗa. Ta ce, "Saboda Yahweh ya ji cewa ba a ƙauna ta, saboda haka ya bani wannan ɗan kuma," ta kuma kira sunansa Simiyon. 34 Daga nan ta sake ɗaukan ciki ta haifi ɗa. Ta ce, "Yanzu a wannan lokacin mijina zai haɗe da ni, saboda na haifa masa 'ya'ya maza uku." Saboda haka a ka kira sunansa Lebi. 35 Ta sake ɗaukar ciki ta kuma haifar ɗa. Ta ce, "Wannan lokacin zan yabi Yahweh." Saboda haka ta kira sunansa Yahuda; Daga nan ta tsaya da haihuwar 'ya'ya.