Sura 18

1 Yahweh ya bayyana ga Ibrahim a gefen itatuwan rimi na Mamre a lokacin da yake zaune a ƙofar rumfa da tsakar rana. 2 Ya duba sama, sai ga mutane uku na tsaye kewaye da shi. Da ya gan su, sai ya ruga daga ga ƙofar rumfar domin ya gamu da su, ya sunkuya ƙasa. 3 Ya ce, "Ubangiji, in na sami tagomashi a wurin ka, kada ka wuce ka rabu da bawanka. 4 Sai a kawo maku ɗan ruwa, ku wanke ƙafafu, ku kuma shaƙata a ƙarƙashin itace. 5 Sai in kawo maku abinci domin ku sami ƙarfi tun da kun zo wurin bawanku. "Suka amsa, Ka yi kamar yadda ka ce." 6 Sai Ibrahim ya yi hanzari ya shiga rumfa wurin Saratu, ya ce, "Hanzarto ki samo awo uku na gãri ki cuɗa shi ki yi gurasa." 7 Sai Ibrahim ya ruga garke ya ɗauko ɗan maraƙi ƙosasshe ya ba bayinsa su yi sauri su gyara shi. 8 Ya ɗauki curin da madara da maraƙin da aka gyara ya kai musu ya tsaya a gefensu a lokacin da suke ci. 9 Suka ce da shi, "Ina Saratu matarka?" Ya amsa, Ta na can, cikin rumfa," 10 Ya ce, hakika zan komo wurinka baɗi war haka, kuma duba, Saratu matarka za ta sami ɗa." Saratu tana ji a bakin ƙofa cikin rumfa dake bayansa. 11 To Ibrahim da Saratu sun tsufa, shekarunsu sun yi nisa sosai, Saratu kuma ta wuce lokacin da mata ke iya haifar 'ya'ya. 12 Domin haka Saratu ta yi wa kanta dariya, tana cewa da kanta, "Bayan na tsufa, shugabana kuma ya tsufa, ko zan sami wannan jin daɗin?" 13 Yahweh yace da Ibrahim, "Meyasa Saratu ta yi dariya ta kuma ce, "Ko hakika zan iya haifar ɗa Yanzu dana tsufa"? 14 Ko akwai abin da ke da wuya ne ga Yahweh? A daidai lokacin dana sa, kamar war haka, zan komo wurinka a shekara mai zuwa Saratu za ta sami ɗa," 15 Sai Saratu ta yi musu, ta ce "Ban yi dariya ba domin tana jin tsoro. Ya amsa mata ya ce, "A'a, kin yi dariya." 16 Sai mutanen suka tashi suka tashi suka duba wajen Sodom. Sai Ibrahim ya tafi tare dasu ya raka su a kan hanyarsu. 17 Amma Yahweh yace "Ko zan ɓoye wa Ibrahim abin da zan aikata, 18 da yake Ibrahim zai zama babbar al'umma kuma dukkan al'umman duniya zasu sami albarka ta wurinsa? 19 Domin na zaɓe shi domin ya umarci 'ya'yansa da gidansa dake biye da shi domin su bi tafarkin Yahweh, su aikata adalci da aikin adalci, domin Yahweh ya cika abin da ya faɗa wa Ibrahim zai aikata a gare shi." 20 Daga nan sai Yahweh yace, "Saboda kukan Sodom da Gomora ya yi yawa, kuma zunubinsu ya haɓaka, 21 Yanzu zan sauka in ga kukan da ake yi a kan su wanda ya zo gare ni, ko hakika sun aikata al'amarin. In ba haka ba zan sani." 22 To sai mazajen suka juya daga can, suka nufi wajen Sodom, amma Ibrahim ya tsaya a gaban Yahweh. 23 Sai Ibrahim ya matso ya ce "Ko zaka share adalai tare da mugaye? 24 In a ce za a sami adalai hamsin a cikin birnin. Ko zaka hallaka shi ba tare da la'akari da adalan nan hamsin ba dake can? 25 Ba zai yiwu ba ka yi haka wato ka kashe adalai tare da miyagu, domin a hori adalai kamar yadda aka hori miyagu. Ba zai yiwu ba mai hukunta duniya ya yi abin da ke dai-dai?" 26 Yahweh yace, "In na sami adalai hamsin a cikin birnin Sodom, to zan kuɓutar da dukkan birnin saboda su." 27 Ibrahim ya amsa ya ce, "Duba na jawo wa kaina magana da Ubangijina, koda yake ni ƙura ne kawai da toka! 28 To in ace adalan sun gaza hamsin ba mutum biyar? Zaka hallaka birnin saboda rashin biyar?" Daga nan sai ya ce, "Ba zan hallaka shi ba, in na sami mutane arba'in da biyar." 29 Sai ya sake yi masa magana, ya ce "To a ce za a sami arba'in a can fa?" Ya amsa, "Saboda mutane arba'in ɗin ba zan yi ba." 30 "Ya ce, "Har yanzu dai ina roƙo Ubangiji kada ka yi fushi in na yi magana. To in a ce za a sami talatin a can fa." Ya amsa ba zai yi hakan ba, in a kwai mutane talatin a can." 31 Ya ce "Ga shi na dage in yi magana da Ubangijina! In a ce za a sami ashirin a can fa." Ya amsa "Saboda mutane ashirin ɗin ba zan hallakar da shi ba." 32 Ya ce, "Ina roƙo kada ka yi fushi, Ubangiji, zan sake faɗin wannan karo na ƙarshe. In a ce za a sami goma fa a can." Sai ya ce, "Ba zan hallaka shi ba saboda mutane goman nan." 33 Sai Yahweh ya tafi a lokacin da ya gama yin magana da Ibrahim, shi kuma Ibrahim ya koma gida.