Sura 17

1 Da Ibram ya kai shekaru tasa'in da tara, lokacin da Yahweh ya bayyana a gare shi ya kuma ce masa, "Ni ne Allah mai iko dukka. Ka yi tafiya a gabana ka zama da rashin laifi. 2 Daga nan zan cika alƙawarina tsakani na da kai, zan kuma kuma ruɓanɓanya ka sosai." 3 Ibram ya sunkuyar da fuskarsa ƙasa sai Allah ya yi magana da shi cewa, 4 "Ni kam, duba, alƙawarina na tare da kai. Zaka zama uban al'ummai masu yawa. 5 Ba za a ƙara kiran sunanka Ibram ba, amma sunanka zai zama Ibrahim - domin na zaɓe ka ka zama uban al'ummai masu yawa. 6 Zan sa ka ruɓanɓanya sosai, daga cikinka kuma zan samar da al'ummai, daga cikinka kuma za a sami sarakuna. 7 Zan kafa alƙawarina tsakanina da kai da kuma zuriyarka dake biye da kai, a dukkan tsararrakinsu domin alƙawari na har abada, in zama Allah a gare ka da kuma zuriyarka dake biye da kai. 8 Zan bada ƙasar da kake zama gare ka da kuma zuriyarka, dukkan ƙasar Kan'ana domin ta zama mallakarka ta har abada, zan kuma zama Allahnsu." 9 Sai Allah yace wa Ibrahim, "Amma kai dole ka kiyaye alƙawarina, da kai da zuriyarka dake biye da kai a dukkan tsararrakinsu. 10 Wannan shi ne alƙawarina da dole zaka kiyaye, tsakanina da kai da dukkan tsararrakin dake biye da kai: 11 Dole ka yi wa kanka kaciya, kuma wannan nan zai zama alamar alƙawarina da kai. 12 Kowanne ɗa namiji a cikinku da ya kai shekaru takwas, dole ne a yi masa kaciya, a dukkan tsararrakin mutanenka. Wannan ya haɗa da wanda aka haifa a gidanka, da kuma wanda aka saya da kuɗinka daga kowanne irin bãƙo wanda ba ya cikin zuriyarka. 13 Da wanda aka haifa maka da wanda ka saya dole ne ayi masa kaciya. Da haka alƙawarina zai kasance a jikinka domin zama alƙawari na har abada. 14 Duk wani namiji wanda ba shi da kaciya za a fitar da shi daga cikin mutanensa. Ya karya alƙawarina." 15 Allah yace da Ibrahim, "Game da Sarai matarka kuma Kada ka ƙara kiranta Sarai. A maimakon Sarai za a kira sunanta Saratu. 16 Zan albarkace ta, kuma za ta zama uwar al'ummai. Sarakunan mutane za su fito daga cikinta." 17 Daga nan sai Ibrahim ya sunkuyar da fuskarsa ƙasa ya yi dariya, a cikin zuciyarsa ya ce, "Ko za a haifa wa ɗan shekara ɗari ɗa? Ta yaya Saratu wadda ta kai shekaru tasa'in za ta iya haifar ɗa?" 18 Ibrahim yace da Allah, "Ah Isma'ila zai zauna tare da kai!" 19 Allah yace, "A 'a, amma Saratu matarka za ta haifa maka ɗa, kuma za ka ba shi suna Ishaku. Zan kafa alƙawarina da shi wato alƙawari na har abada da zuriyarsa dake biye da shi. 20 Shi kuma Isma'ila na ji ka. Duba na sa masa albarka, zan kuma ruɓaɓɓanya shi zan wadata shi sosai. Zai zama uban kabilu goma sha biyu. Zan kuma mai da shi babbar al'umma. 21 Amma alƙawarina zan kafa shi da Ishaku, wanda Saratu za ta haifa maka baɗi war haka." 22 Da ya gama yi masa magana, sai Allah ya rabu da Ibrahim. 23 Sai Ibrahim ya ɗauki Isma'ila ɗansa, da duk waɗanda aka haifa a cikin iyalinsa, da duk waɗanda ya saya da kuɗinsa da dukkan mazaje na mutanensa duk suka yi kaciya a rana ɗaya kamar yadda Allah ya faɗa masa. 24 Ibrahim yana da shekaru tasa'in da tara lokacin da ya yi kaciya. 25 Ɗansa Isma'ila kuma yana da shekaru sha uku a lokacin da aka yi masa kaciya. 26 A wannan ranar aka yi wa Ibrahim da ishaku kaciya a rana ɗaya. 27 Aka yi masa kaciya tare da dukkan mazajensa, da waɗanda aka haifa masa da waɗanda ya saya da kuɗi daga bãƙi.