Sura 16

1 To Sarai, matar Ibram, ba ta haifa masa 'ya'ya ba tukuna, amma tana da baiwa, mutumiyar Masar, sunanta Hajara. 2 To sai Sarai ta ce da Ibram, "Duba Yahweh ya hana mani 'ya'ya, ka je ka kwana da baiwata. Watakila na sami 'ya'ya ta wurinta." Ibram ya saurari muryar Sarai. 3 Bayan Ibram ya yi shekaru goma a Kan'ana ne Sarai ta miƙa baiwarta Hajara ga Ibram a matsayin mata. 4 Sai ya yi tarayya da Hajara ta kuwa yi juna biyu. Da taga ta yi juna biyu sai ta fara duban uwargijiyarta da reni. 5 Daga nan Sarai ta ce da Ibram, "Wannan kuskuren a kaina saboda kai ne. Na bada baiwata gare ka, kuma bayan ta ga ta yi juna biyu, sai aka sayar da ni a idonta. Bari Ubangiji ya shari'anta tsakanina da kai." 6 Amma Ibram yace da Sarai, "Duba ita baiwarki ce, tana ƙarƙashin ikonki, ki yi mata abin da kike tunanin ya fi kyau," Sai Sarai ta takura mata sosai, sai ta gudu daga gare ta 7 Sai mala'ikan Yahweh ya same ta a maɓulɓular ruwa a jeji, wannan maɓulɓular dake kan hanya zuwa Shur. 8 Ya ce da ita, Hajara baiwar Sarai daga ina ki ka zo kuma ina za ki? sai ta ce "ina gujewa uwargijiyata ne Sarai." 9 Mala'ikan Yahweh yace da ita, "Ki koma wurin uwargiyarki, ki miƙa kai ga shugabancinta." 10 Sai mala'ikan Yahweh yace da ita, "Zan ruɓanɓaya zuriyarki sosai, domin su zama da yawa, su wuce ƙirge." 11 Hakanan mala'ikan Yahweh yace da ita, Duba kina ɗauke da juna biyu na ɗa namiji, kuma za ki kira sunansa Isma'ila, saboda Yahweh ya ji ƙuncinki. 12 Zai zama jakin jeji, zai yi magaftaka da dukkan mutane, dukkan mutane kuma na gãba da shi, zai kuma zauna a ware da 'yan, uwansa." 13 Sai ta bada wannan sunan ga Yahweh wanda ya yi magana da ita, "Kai Allah ne mai ganina," domin ta ce, "Ko zan ci gaba da gani, bayanda ya gan ni?" 14 Saboda haka ake kiran rijiyar Beyer Lahai Roi; tana nan tsakanin Kadesh da Bered. 15 Hajara ta haifa wa Ibram ɗa namiji ta ba shi suna Isma'ila. 16 Ibram na da shekaru tamanin da shida a lokacin da Hajara ta haifi Isma'ila.