Sura 15

1 Bayan waɗannan abubuwa sai maganar Yahweh ta zo wurin Ibram a wahayi, cewa, "Ibram kada ka ji tsoro ni ne garkuwarka da kuma babban ladanka." 2 Ibram yace, ya Ubangiji Yahweh, me za ka bani tunda yake har yanzu bani da ɗa. Magajin gidana kuma Eliyazar ne daga Damaskus," 3 Ibram yace, da yake baka bani zuriya ba, duba, ɗan aikin gida ne ya zama magajina. 4 Sai ga maganar Yahweh ta zo gare shi, cewa "Ba wannan mutumin ne zai gaje ka ba, amma wanda zai fito daga cikin jikinka ne zai zama magajinka." 5 Daga nan sai ya fito da shi waje ya ce, "Duba sama, ka kuma ƙidaya taurari, in za ka iya ƙirga su. Daga nan ya ce da shi, haka zuriyarka za ta zama." 6 Ya yi imani da Yahweh, sai ya lisafta masa shi a matsayin adalci. 7 Ya ce da shi, "Ni ne Yahweh, wanda ya fito da kai daga Ur ta Kaldiyawa, domin in baka wannan ƙasar ka gãje ta." 8 Ya ce ya Ubangiji Yahweh, ta yaya zan sani cewa zan gãje ta?" 9 Daga nan ya ce da shi, "Ka kawo mini bijimi ɗan shekara uku da kuma akuya 'yar shekara uku da kurciya, da tantabara." 10 Ya kawo masa dukkan waɗannan ya kuma datsa su biyu-biyu ya kuma ajiye kowanne tsagi a gefen ɗayan, amma bai raba tsuntsayen ba. 11 Lokacin da tsuntsayen dake yawo suka zo wurin mushen sai Ibram ya kore su. 12 Daga nan bayan rana ta kusa faɗuwa, Ibram ya yi barci mai nauyi, sai ga wani babban duhu mai ban razana ya sha kan shi. 13 Daga nan Yahweh yace da Ibram, hakika ka san cewa zuriyarka zasu yi baƙunci a ƙasar da ba tasu ba, za a kuma bautar da su, a tsananta musu har tsawon shekaru ɗari huɗu. 14 Zan hukunta waccan al'ummar da zasu bauta wa, bayan haka kuma zasu fita da mallaka mai yawa. 15 Amma za ka je wurin ubanninka da salama, kuma za a yi maka jana'iza a shekaru ma su kyau. 16 A cikin tsara ta huɗu zasu sake zuwa nan kuma, saboda muguntar Amoriyawa ba ta kai iyakarta ba tukuna." 17 Da rana ta faɗi dare kuma ya yi, sai ga hayaƙin wuta da kuma harshen wutar tukunya da tartsatsi suka wuce a tsakanin yankin naman. 18 A wannan lokaci Yahweh ya yi yarjejeniya da Ibram cewa ga zuriyarka zan bada wannan ƙasa tun daga kogin Masar zuwa babban kogin Yuferetis- 19 da Kan'aniyawa da Kanizitawa 20 da Hitiyawa da Feriziyawa da Refatiyawa, 21 da Amoriyawa da Kan'aniyawa da Girgashiyawa da Yebusiyawa."