Sura 14

1 Sai ya zamana a kwanakin Amrafel, sarkin Shinar, Ariyok sarkin El'asar, Kedorlaoma sarkin Elam, da Tidal sarkin Goyim, 2 suka kai yaƙi kan Bera sarkin Sodom, Birsha, sarkin Gomora, Shinab, sarkin Adma, Shemebar, Sarkin Zeboyim, da sarkin Bela (wato wanda ake kira Zowar). 3 Waɗancan sarakuna na baya suka taru a kwarin Siddim (wanda kuma ake kira Tekun Gishiri). 4 Suka bautawa Kedorlawoma shekaru sha biyu, amma a shekara tasha uku suka yi tayawe. 5 A shekara ta sha huɗu kuma, da sarakunan dake tare da shi suka zo suka kawo hari kan Rafaim a Ashterot Karnaim, da Zuzim a Ham, na Emim a Shaba Kiriataim, 6 da Horitiyawa a ƙasar duwatsu ta Se'ir, har zuwa El Faran dake kusa da hamada. 7 Daga nan sai suka juyo suka zo En Mishfat (wadda kuma ake kira Kadesh), suka cinye dukkan ƙasar Amelikawa, da kuma ta Amoriyawa waɗanda ke zama a Hazazon Tamar. 8 Daga nan sai sarkin Sodom, da sarkin Gomora, da sarkin Admah da sarkin Zeboim da sarkin Bela (da ake kira Zowar) suka je suka yi shirin yaƙi 9 găba da Kedorlawomar sarkin Elam, Tidal, sarkin Goim, Amrafel sarkin Shinar, Ariok, sarkin Ellasar; sarakuna huɗu găba da biyar. 10 To kwarin Siddim ya cika da ramukan yaƙi, da sarakunan Sodom da Gomora suka gudu sai suka faɗa cikinsu a can. Waɗanda suka rage suka gudu kan duwatsu. 11 Domin haka maƙiya suka kwashe dukkan kayayyakin Sodom da Gomora suka tafi abin su 12 Da suka tafi, suka kame Lot, ɗan ɗan'uwan Ibram, wanda ke zama a Sodom tare da dukkan malakarsa. 13 Wani da ya tsira ya zo ya gaya wa Ibram Ba'ibirane. Yana zama a gefen rimin Mamre Ba'amore, ɗan'uwan Eshkol da Aner, Waɗanda dukkansu abokan Ibram ne. 14 To da Ibram ya ji maƙiya sun kame ɗan'uwansa, sai ya jagoranci horarrun mazajensa guda 318 waɗanda aka haifa a gidansa ya bi su har zuwa Dan. 15 Ya rarrraba mazajensa găba da su a wannan daren ya kai masu hari, ya bi su har zuwa Hoba wadda ta ke arewa da Damaskus. 16 Daga nan ya dawo da dukkan mallakar, ya kuma dawo da ɗan'uwansa Lot da duk kayansa, da mataye da sauran mutane. 17 Bayan Ibram ya dawo daga yin nasara da Kedorlawoma da sarakunan dake tare da shi, sarkin Sodom ya tafi ya tare shi a kwarin Shabe (Wanda kuma ake kira Kwarin Sarki) 18 Melkizedek, sarkin Salem ya kawo gurasa da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Maɗaukaki. 19 Ya albarkace shi cewa, Mai albarka ne Ibram ta wurin Allah Mafi Ɗaukaka, Mahallicin sama da duniya. 20 Albarka ta tabbata ga Allah Mafi Ɗaukaka, wanda ya bada maƙiyanka a hannunka." Sai Ibram ya ba shi kaso ɗaya bisa goma na komai. 21 Sarkin Sodom yace da Ibram, "Ka bani mutane, ka ɗauki kayayyakin domin kanka. 22 "Ibram yace da sarkin Sodom, "Na ɗaga hannunna sama zuwa ga Yahweh, Allah Maɗaukaki, Mahallicin sama da duniya, 23 cewa ba zan ɗauki koda tsinkin zare ko takalmi ko dukkan wani abu dake naka ba, domin kada ka ce, 'Na sa Ibram ya azurta,' 24 Ba zan ɗauki komai ba sai abin da matasa samari suka ci da kuma rabon mazajen dake tare da ni. Let Aner, Eshkol, da Mamre su ɗauki nasu kason."