Sura 13

1 Sai Ibram ya bar Masar ya tafi Negeb, shi da matarsa da duk abin da ya mallaka. Lot ya tafi tare da su. 2 Ibram ya wadata sosai ta fannin dabbobi da zinariya da azurfa. 3 Ya ci gaba da tafiya daga Negeb har zuwa wurin da ya kafa rumfarsa a dã baya, tsakanin Betal da Ai. 4 Ya tafi har zuwa inda ya kafa rumfa a baya. A nan ya fara kiran sunan Yahweh. 5 To Lot wanda ke tare da Ibram shi ma yana da garke da sauran bisashe da rumfuna. 6 Ƙasar kuma ta yi masu kaɗan, su da mallakarsu domin suna da mallaka da yawa, saboda haka ba su iya tsayawa a wuri ɗaya ba. 7 Hakanan akwai rashin jituwa tsakanin makiyayan dabbobin Ibram da kuma makiyayan dabbobin Lot. Feriziyawa da Kan'aniyawa ne ke zama a wannan ƙasar a wancan lokacin. 8 Sai Ibram yace da Lot, "bai kamata a sami rashin jituwa tsakanina da kai ba, ko kuma tsakanin makiyayan dabbobina da makiyayan dabbobinka. 9 Fiye ma da haka mu dangi ne, duba ba fili ne nan gabanka ba? Ka zaɓi duk inda kake so, in ka zaɓi hagu, ni sai in zaɓi dama, in ka zaɓi dama ni sai in zaɓi hagu" 10 Sai Lot ya duba yankin Yodan, ya kuma gan shi kore shar har zuwa yankin Zowar, kamar lambun Yahweh, kamar kuma ƙasar Masar. Haka yake kafin a hallaka Sodom da Gomora. 11 Sai Lot ya zaɓi wannan filin na Yodan ya tafi gabas, dangin suka rabu da juna. 12 Ibram ya zauna a ƙasar Kan'ana Lot kuma ya zauna a biranen filin ƙasa. Ya kakkafa rumfunansa har zuwa Sodom, 13 To mutanen Sodom miyagu ne sosai, masu yi wa Yahweh zunubi ne. 14 Yahweh yace da Ibram bayan Lot ya rabu da shi. "Duba daga inda kake tsayuwa zuwa arewa, kudu da gabas da yamma. 15 Dukkan wannan ƙasar da ka ke gani, na bada ita ga zuriyarka har abada. 16 Zan haɓaka zuriyarka ta zama kamar turɓayar ƙasa, domin in har mutum zai iya ƙirga turɓayar ƙasa to zai iya ƙirga zuriyarka. 17 Tashi ka kewaya faɗin ƙasar da tsawonta, domin zan bada ita gare ka. 18 Sai Ibram ya tashi ya ɗauki rumfarsa ya je ya zauna kusa da itatuwan rimayen Mamre, wanda ke a Hebron. A can ya kafa bagadi domin Yahweh.