Sura 12

1 Sai Yahweh yace da Ibram "Ka tashi ka bar ƙasarka da danginka, da kuma ƙasar mahaifinka, zuwa ƙasar da zan nuna maka, 2 zan maishe ka babbar al'umma, zan albarkace ka in kuma sa sunanka ya yi girma, kuma za ka zama albarka. 3 Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, zan kuma la'anta duk wanda ya tozarta ka. Ta wurin ka dukkan al'ummar duniya za ta sami albarka." 4 To Ibram ya tafi, kamar yadda Yahweh ya faɗa masa ya yi, Lot kuma ya tafi tare da shi. Ibram yana da shekaru saba'in da biyar a lokacin da ya tafi ya bar Haran. 5 Ibram ya ɗauki matarsa Sarai, da Lot ɗan ɗan'uwansa da dukkan mallakarsu da suka tara, da kuma dukkan mutanen da suka samu a Haran. Suka tafi zuwa ƙasar Kan'ana, suka kuwa isa ƙasar Kan'ana. 6 Ibram ya wuce ƙasar har zuwa Shekem, zuwa al'ul na Moreh. A wancan lokacin Kan'aniyawa na zaune a ƙasar. 7 Yahweh ya bayyana ga Ibram, ya ce, "Ga zuriyarka Zan ba da wannan ƙasa." Daga nan Ibram ya gina bagadi domin Yahweh, wanda ya bayyana a gare shi. 8 Daga can ya tafi zuwa ƙasar duwatsu a gabashin Betal, inda ya kafa rumfarsa, ga Betal a yammaci, Ai kuwa a gabashi. A can ya kafa bagadi domin Yahweh, ya kuma yi kira bisa sunan Yahweh. 9 Daga nan Ibram ya ci gaba da tafiya, zuwa wajen Negeb. 10 A kwai yunwa a cikin ƙasar, don haka Ibram ya gangara zuwa Masar ya zauna domin yunwar ta tsananta sosai a cikin ƙasar. 11 Da ya kusa shiga Masar sai ya ce da matarsa Sarai, "Duba na san ke mace ce kyakkyawa. 12 In Masarawa suka gan ki za su ce, 'Wannan matarsa ce; za su kuma kashe ni, amma za su bar ki da rai. 13 Ki ce ke 'yar'uwata ce, domin komai ya yi mani dai-dai saboda ke, don a bar ni in rayu saboda ke." 14 Sai ya zamana bayan Ibram ya shiga cikin Masar, Masarawa suka ga cewa Sarai kyakkyawa ce. 15 'Ya'yan sarki suka gan ta, suka kuma yaba mata a gaban Fir'auna, sai aka ɗauki matar zuwa gidan sarki. 16 FIr'auna ya kyautatawa Ibram saboda ita, ya ba shi tumaki, takarkarai, da jakai maza da mata da bayi maza da mata da kuma raƙuma. 17 Sai Yahweh ya bugi gidan Fir'auna da annoba mai zafi saboda Sarai matar Ibram. 18 Fir'auna ya kira Ibram ya ce da shi me kenan ka yi mini? Meyasa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ba ce? 19 Meyasa ka ce ita 'yar'uwarka ce; don in ɗauke ta ta zama matata? To yanzu ga matarka nan. Ka ɗauke ta ku tafi." 20 Sai Fir'auna ya bada umarni game da shi daga nan suka sallame shi ya tafi, tare da matarsa da duk abin da yake da shi.