Sura 19

1 Mala'ikun guda biyu suka zo Sodom da yamma, a lokacin da Lot ke zaune a ƙofar Sodom. Da Lot ya gan su sai ya tashi ya tare su, ya sunkuyar da fuskarsa har ƙasa. 2 "Ya ce, "Ya shugabannina, ina roƙon ku daku biyo ta gidan baranku, ku kwana ku wanke ƙafafunku. Da safe sai ku tashi ku yi tafiyarku." Suka amsa, "A'a za mu je mu kwana a kwararo." 3 Amma ya yi ta roƙon su, sai suka tafi tare da shi, suka shiga gidansa. Ya shirya musu abinci ya kuma soya musu gurasa marar gami suka ci. 4 Amma kafin su kwanta, mazajen birnin, wato mazajen Sodom, suka kewaye gidan, da tsofaffinsu da matasansu, da dukkan mazajen birnin. 5 Suka kira Lot, suka ce da shi, "Ina mutanen da suka zo gidanka yanzu? Fito da su gare mu, domin mu kwana da su." 6 To sai Lot ya fita wajen ƙofa ya kulle ƙofar a bayansa. 7 Ya ce da su, "Ina roƙon ku 'yan'uwana, kada ku yi aikin mugunta irin wannan. 8 Duba ina da 'ya'ya mata guda biyu da ba su taɓa kwana da maza ba. Ina roƙon ku in kawo muku su, ku yi duk abin da kuka so da su. Amma kada ku yi wa mazajen nan komai, domin suna nan ne a ƙarƙashin kulawata 9 Suka ce, "Ka tsaya can!" Haka kuma suka ce, "Shi da ya zo baƙunta, yanzu kuma ya zama alƙalinmu! Yanzu za mu ci mutuncika fiye da yadda za mu yi musu." Suka matsa wa Lot da kuma mutanen, suka zo kusa da ƙofar domin su ɓarke ta. 10 Amma sai mutanen suka miƙa hannuwansu suka shigo da Lot ciki suka kulle ƙofar. 11 Sai bãƙin na Lot suka bugi mutanen da makanta, wato mutanen dake wajen ƙofar gidan, duk da matasansu da tsofaffinsu duk ƙarfinsu ya ƙare a lokacin da suke ƙoƙarin ɓarke ƙofar 12 Sai mutanen suka ce da Lot, "Ko kana da wani naka a nan? Ko surukai, ko 'ya'ya maza da mata da duk wanda kake da shi a cikin birnin, ka fitar da su daga birnin nan. 13 Domin mu na gab da hallaka wannan wurin, saboda zargin da ake yi wa birnin a gaban Yahweh ya yi yawa shi ya sa ya aiko mu domin mu hallaka shi." 14 Sai Lot ya tafi ya yi magana da surukansa, wato mazajen da suka yi alƙawari zasu auri 'ya'yansa mata, ya ce "Ku hanzarta, ku fita daga wannan wurin, domin Yahweh na gab da hallaka birnin." Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi. 15 Da safiya ta yi, mala'ikun suka hanzarta Lot, "Ka fito da kai da matarka da 'ya'yanka mata guda biyu dake a wannan wuri, domin kada a share ku tare a cikin wannan hukunci na birni." 16 Amma ya yi jinkiri. Sai mazajen suka kama hannuwansa, da hannun matarsa, da hannuwan 'ya'yansa mata guda biyu, saboda Yahweh ya yi masa jinƙai. Suka fitar dasu bayan birnin. 17 Da suka fitar dasu waje, ɗaya daga cikin mazajen ya ce, "Ku tserar da rayukanku! Kada ku waiga baya, ko kuma ku tsaya a wannan filin. Ku gudu kan duwatsu domin kada a hallakar da ku." 18 Lot yace da su, "A'a shugabannina ina roƙon ku! 19 Baranku ya sami tagomashi a wurinku, kuma kun nuna mini kirki sosai da kuka ceci raina, amma ba zan iya kai wa kan duwatsu ba, masifar za ta same ni, kuma zan mutu. 20 Duba ga wani birni can, ya isa in je can domin tsira, kuma ƙarami ne, ina roƙo ku bar ni in je can in tsira (ba ɗan ƙarami ba ne?), rayuwata kuma za ta cetu." 21 Ya ce da shi, "Shikenan, na biya maka wannan buƙata, kuma ba zan hallaka birnin da ka faɗa ba. 22 Ka yi hanzari ka gudu can, domin ba zan yi wani abu ba sai ka isa can." Shi ya sa ake kiran wurin Zowar. 23 Rana ta ɗaga bisa duniya a lokacin da Lot ya isa Zowar. 24 Sai Yahweh ya saukar da ruwan wuta da matsanancin zafi bisa Sodom da Gomora. 25 Ya hallaka waɗannan biranen, da filayen, da duk mazauna biranen da tsire-tsire da suka yi girma a ƙasa. 26 Amma matar Lot dake bayansa, ta waiwaya baya, sai ta zama umudin gishiri. Ibrahim ya tashi da sassafe ya je wurin da ya tsaya tare da Yahweh. 27 Ya duba wajen Sodom da Gomora da kuma dukkan filayen. 28 Da ya duba sai ya ga hayaƙi na tashi daga filin kamar na hayaƙin matoya. 29 To lokacin da Allah ya hallakar da biranen da filayen, Allah ya tuna da Ibrahim Ya fitar da Lot daga wannan hallakarwar a lokacin da ya hallaka biranen da Lot ya zauna. 30 Amma Lot ya fita daga Zowar zuwa duwatsu tare da 'ya'yansa mata guda biyu, domin yana jin tsoron zama a Zowar. Sai ya zauna a cikin kogon dutse, shi da 'ya'yansa mata guda biyu. 31 Babbar ta ce da ƙaramar, "Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wanda zai kwana damu bisa ga tsarin dukkan duniya. 32 Ki zo, mu sa mahaifinmu ya sha ruwan inabi ya bugu, sai mu kwana da shi, domin mu wanzar da sunan mahaifinmu." 33 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi ya bugu a wannan daren. Sai babbar ta je ta kwana da mahaifinta, bai ma san lokacin da ta kwanta ba, bai kuma san lokacin da tashi ba. 34 Washegari Sai babbar ta ce da ƙaramar, "Kin ga, jiya na kwana da mahaifina. Yau kuma sai mu sa shi ya sake buguwa da ruwan inabi, ke kuma sai ki je ki kwana da shi, domin mu wanzar da sunan mahaifinmu." 35 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi ya bugu, sai ƙaramar ta je ta kwana da shi. Bai san lokacin da ta kwanta ba haka kuma bai san lokacin da ta tashi ba. 36 Ta haka 'ya'yan Lot guda biyu suka yi juna biyu ta wurin mahaifinsu. 37 Ta farin ta haifi ɗa namji ta sa masa suna Mowab. Shi ne ya zama uban Mowabawa a yau. 38 Ita ma ƙaramar 'yar ta haifi ɗa namiji sai ta ba shi suna Ben Ammi. Shi ne ya zama uban mutanen Ammon na yau.