Genesis 15

Genesis 15:1

Bayan waɗannan abubuwa

"Waɗannan abubuwa" na nufin lokacin yaƙin sarakunan da kuma ceton da Ibram ya wa Lot.

maganar Yahweh ta zo

Wannan na nufin cewa Yahweh ya yi magana. AT: "Yahweh ya faɗa saƙonsa" (Duba: /WA-Catalog/ha_tm?section=translate#figs-idiom)

maganar Yahweh

Anan "magana" na wakiltar saƙon Yahweh ne. AT: "saƙon Yahweh" (Duba: /WA-Catalog/ha_tm?section=translate#figs-metonymy)

garkuwa ... babban ladanka

Allah yayi amfani da waɗannan kalmomi domin ya bayana wa Ibram halinsa da kuma dagantakarsa da Ibram. (Duba: /WA-Catalog/ha_tm?section=translate#figs-metaphor)

lada

"biya." Wani na nufin biyan da wani ya cancanta. mai yiwuwa ma'ana biyu ne 1) "Ni ne kadai ka ke bukata" ko 2) Zan ba ka dukka abin da ka ke bukata."

Ibram yace da ya ke ka ba ni

"Ibram ya ci gaba da cewa, da ya ke ka ba ni"

Genesis 15:4

Sai gashi

Kalamar "gashi" na jadada cewa kalmar Yahweh ta sa ke zuwa ga Ibrahim.

Wannan mutumin

Wannan na nufin Eliyaza ne daga Damaskus.

wanda zai fito daga cikin jikinka

"wanda za ka zama mahaifinsa" ko "asalin ɗan ka." Ɗan Ibram zai zama magajin sa.

ƙidaya taurari

'ƙirga taurari"

haka zuriyarka za ta zama

Kamar yanda Ibram ba zai iya ƙidaya taurari ba, haka nan ba zai iya ƙidaya zuriyarsa ba domin za su kasance da yawa.

Genesis 15:6

Ya yi imani da Yahweh

Wannan na nufi ya amince cewa abin da Yahweh ya faɗa gaskiya ne.

ya lisafta masa shi a kan adalci

"Yahweh ya lisafta imanin Ibram a kan adalci" ko "Yahweh ya ɗauke Ibram adali ne domin Ibram ya gaskanta da shi"

Ni ne Yahweh, wanda ya fito da kai daga Ur

Yahweh na tunar da Ibrahim game da abin da ya riga ya yi domin Ibrahim ya san cewa Yahweh na da ikon ba wa Ibram abin da ya alkawatar masa.

gãje ta

"same ta" ko "domin ka mallake ta"

ta yaya zan sani

Ibram na tambaya domin ya kara samun tabbaci cewa Yahweh zai ba shi kasar.

Genesis 15:9

mushen

"jikin dabbobi da tsunstayen da suka mutu"

Ibram ya kore su

"Ibram ya kore tsuntsayen." Ya tabbatar cewa tsuntsaye ba su ci dabbobin da suka mutu ba.

Genesis 15:12

Ibram ya yi barci mai nauyi

Wannan ƙarin magana ne. AT: "Ibrahim ya yi barci mai zurfi" (Duba: /WA-Catalog/ha_tm?section=translate#figs-idiom)

wani babban duhu mai razana

"matsananciyar duhu da ta razanar da shi"

lullube shi

"mamaye shi"

baƙi

"'yan ƙasan waje" ko "wanda ba 'yan gida ba"

a bautar da su a kuma tsananta musu

Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "masu ƙasar kuwa za su maishe zuriyarka bayi, su kuma tsananta musu" (Duba: /WA-Catalog/ha_tm?section=translate#figs-activepassive)

Genesis 15:14

Muhimmin Bayani:

Yahweh ya ci gaba da yi wa Ibram maganar sa'ad da Ibram yana cikin mafarkin.

Zan hukunta

Anan "hukunta" na nufin abin da zai faru bayan Allah ya yi shari'a. AT: "Zan azabtar" (Duba: /WA-Catalog/ha_tm?section=translate#figs-metonymy)

mallaka mai yawa

Wannan karin magana ne. AT: "mallaka mai matuƙan yawa" ko "wadatar dukiya" (Duba: /WA-Catalog/ha_tm?section=translate#figs-idiom)

za ku je wurin ubanninku

Wannan wata hanya ɗabi'a ne na cewa "za ku mutu." (Duba: /WA-Catalog/ha_tm?section=translate#figs-euphemism)

za a yi maku jana'iza a shekaru ma su kyau

"za ku tsufa kafin ku mutu, iyalinku kuwa su yi muku jana'iza"

A cikin tsara ta huɗu

Tsara ɗaya a nan na nufi tsawon shekaru ɗari. "bayan shekaru ɗari huɗu"

za su sake zuwa nan

"zuriyarka za su sake dawo nan." Zuriyar Ibrahim za su sake komowa ƙasar da Ibram ke zama, da kuma ƙasar da Yahweh ya alkawatar ma sa.

bai kai matsayinsa ba tukuna

"bai cika ba" ko "sai ya yi muni kafin zan hukunta su"

Genesis 15:17

hayaƙin wuta da kuma harshen wutar tukunya da tartsatsi su ka wuce a tsakanin yankin nama

Allah ya yi wannan domin ya nuna wa Ibram cewa ya na yin yarjejeniya tare shi.

wuce a tsakanin yankin nama

"wuce tsakanin layin naman dabba"

Ina ba da wannan ƙasa

Ta faɗin wannan, Allah na ba da ƙasa wa zuriyar Ibram. Allah na yin haka a wacan lokacin amma zuriyar ba za su shiga ƙasar ba sai bayan shekaru da yawa.

babbban kogin Yuferetis

kogin Yuferetis mai girma.

da Keniyawa, Keniziyawa, Kadmoniyawa, da Hitiyawa, Feriziyawa, Refatiyawa, da Amoriyawa, Kan'aniyawa, Girgashiyawa, da Yebusiyawa

Waɗannan sune sunayen kungiyar mutanen da suke zama a ƙasar. Allah a yardar wa zuriyar Ibrahim su ci nasara yaƙi da waɗannan mutane, su kuma ɗauki ƙasar. (Duba: /WA-Catalog/ha_tm?section=translate#translate-names)