Sura 27

1 Da Ishaku ya tsufa har ta kai ga ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa, babban ɗansa, ya ce da shi, "Ɗana." Ya ce da shi "Ga ni." 2 Ya ce, "Gashi yanzu, na tsufa. Ban kuma san ranar mutuwata ba. 3 Domin haka, ka ɗauki kwarinka da bakanka da makamanka, ka je daji ka yiwo mini farauta. 4 Ka yi mani dage-dage, irin wanda nake ƙauna, ka kawo shi gare ni domin in ci in albarkace ka kafin in mutu." 5 Sai Rebeka ta ji lokacin da Ishaku ke magana da Isuwa ɗansa. Isuwa ya tafi daji domin ya yiwo farauta ya kawo. 6 Sai Rebeka ta yi magana da Yakubu ɗanta ta ce, "Duba, na ji mahaifinka ya yi magana da Isuwa ɗan'uwanka. Ya ce, 7 'Ka farauto mani nama ka shirya mani dage-dage domin in ci in albarkace ka a gaban Yahweh kafin mutuwata.' 8 Yanzu fa ɗana, ka yi biyayya da muryata kamar yadda zan umarce ka. 9 Ka je garke, ka kawo mini "yan awaki guda biyu; zan kuma shirya dage-dage mai daɗi da su domin mahaifinka, kamar yadda yake ƙauna. 10 Zaka kai shi wurin mahaifinka, domin ya ci, ya albarkace ka kafin ya mutu." 11 Yakubu yace da Rebeka mahaifiyarsa, "Gashi, Isuwa ɗan'uwana gargasa ne, ni kuma sulɓi ne. 12 In mahaifina ya taɓa ni, na kuma zama mayaudari a gare shi. Zan jawo wa kaina la'ana ba albarka ba." 13 Mahaifiyarsa ta ce da shi, "Ɗana, bari duk wata la'ana ta auko mani. kai dai ka yi biyayya da muryata, ka je ka kawo su wurina." 14 Sai Yakubu ya tafi ya samo 'yan awaki guda biyu ya kawo su ga mahafiyarsa, mahaifiyarsa kuwa ta shirya dage-dage, kamar yadda mahaifinsa ke ƙauna. 15 Sai Rebeka ta ɗauki tufafin Isuwa babban ɗanta, mafi kyau, wanda ke tare da ita a gida, sai ta sa wa Yakubu, ƙaramin ɗanta. 16 Sai ta sa fatar 'yan awaki a hannunsa da kuma tattausan sashen wuyansa. 17 Sai ta sa dage-dagen mai daɗi da gurasar da ta shirya a hannun ɗanta Yakubu. 18 Sai Yakubu ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, "Mahaifina." Ya ce,"Ga ni nan; Wane ne kai ɗana?" 19 Yakubu yace da mahaifinsa, "Ni ne Isuwa ɗanka na fari; Na yi kamar yadda ka ce da ni. Yanzu sai ka tashi ka zauna ka ci ɗan dage-dagen, domin ka albarkace ni." 20 Ishaku yace da ɗansa, "Ɗana yaya aka yi ka samo shi da sauri haka?" Ya ce, "Domin Yahweh Allanka ya kawo su wurina". 21 Ishaku yace da Yakubu, "Ɗana ka matso kusa da ni, domin in taɓa ka, domin in san ko kai ɗana ne." 22 Yakubu ya matsa ga Ishaku mahaifinsa, Ishaku kuma ya taɓa shi ya ce, "Muyar kamar ta Yakubu ce, amma jikin na 23 Isuwa ne." Ishaku bai iya gane shi ba, domin hannuwansa gargasa ne kamar na hannuwan ɗan'uwansa Isuwa, domin haka Ishaku ya albarka ce shi. 24 Ya ce "Kai ne ɗana Isuwa kuwa?" Ya amsa "Ni ne." 25 Ishaku yace, "Kawo abincin wurina, zan ci in kuma albarkace ka. Yakubu ya kawo abincin gare shi. Ishaku ya ci, Yakubu kuma ya kawo masa ruwan inabi, ya kuwa sha. 26 Sai babansa Ishaku yace da shi, "Ɗana ka zo nan kusa ka sumbace ni." 27 Yakubu ya matso kusa ya sumbace shi' ya sunsuni ƙamshin suturarsa ya albarkace shi. Ya ce, "Duba, ƙamshin ɗana yana kama da ƙamshin ganyayyakin da Yahweh ya sa wa albarka. 28 Allah ya baka rabo na raɓar sama, rabo na sashin ƙasa mafi dausayi, ya baka hatsi da ruwan Inabi mai yawa. 29 Mutane da al'ummai kuma su rusuna maka. Ka zama shugaban 'yan'uwanka maza, 'ya'yan mahaifiyarka maza kuma su rusuna maka. Duk kuma wanda ya la'ance ka ya zama la'annanne, duk wanda kuma ya albarkace ka ya zama mai albarka." 30 Ishaku na gama sa wa Yakubu albarka kenan, bayan ya fita daga wurin mahaifinsa Ishaku, sai ga Isuwa ɗan'uwansa ya shigo daga wurin farautarsa. 31 Shi ma ya shirya dage-dagen, abinci mai daɗi ya kawo shi wurin mahaifinsa. Ya ce da mahaifinsa, "Mahaifina, ka tashi ka ci irin dage-dagen ɗanka, domin ka albarkace ni." 32 Ishaku mahaifinsa ya ce da shi, "Kai wane ne?" Ya ce, "Ni ne ɗan farinka, Isuwa. 33 Ishaku ya gigice sosai ya ce, "Wane ne ya yiwo farauta ya kawo mani dage-dage? Na ci a gabanin zuwanka, na kuma albarkace shi. Hakika, zai zama da albarka." 34 Bayan Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, ya yi kuka da baƙinciki matuƙa, ya ce da mahaifinsa, "Ni ma ka albarkace ni mana, mahaifina." 35 Ishaku yace, "Ɗan'uwanka ya zo cikin yaudara ya karɓe albarkarka." 36 Isuwa yace, "Ashe ba haka ta sa aka ba shi suna Yakubu ba? Domin ya zambace ni sau biyu. Ya karɓe matsayina na ɗan fãri, kuma duba yanzu ya karɓe albarkata." Daga nan ya ce, "Ba ka rage wata albarka domina ba?" 37 Ishaku ya amsa ya ce da Isuwa, "Duba, na maishe shi ya zama shugabanka, kuma na ba shi dukkan 'yan'uwansa maza su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Me kuma zan yi maka, ɗana?" 38 Isuwa yace da mahaifinsa, "Ko albarka ɗaya ba ka rage mani ba mahaifina? Ka albarkace ni nima mahaifina." Isuwa yayi kuka da ƙarfi. 39 Ishaku mahaifinsa ya amsa masa cewa, "Duba, wurin da zaka zauna zai zama da nisa daga wadatar duniya, nesa kuma da raɓar sararin sama. 40 Ta wurin takobinka zaka rayu, kuma zaka bautawa ɗan'uwanka. Amma lokacin da kayi tayarwa, zaka kawar da karkiyarsa daga wuyanka." 41 Isuwa ya ƙi Yakubu saboda albarkar da mahaifinsa ya ba shi. Isuwa yace a cikin zuciyarsa, "Kwanakin makokin mahaifina sun kusa wucewa, bayan wannan zan kashe ɗan'uwana Yakubu." 42 Sai aka faɗa wa Rebeka kalmomin da babban ɗanta ya faɗa. Domin haka ta aika a kira Yakubu ƙaramin ɗanta ta ce da shi, "'Duba, ɗan'uwanka na tunanin yadda zai kashe ka. 43 Saboda haka, ɗana, yanzu sai ka yi biyayya da muryata, ka gudu wurin Laban ɗan'uwana a Haran. 44 Ka zauna tare da shi na ɗan lokaci, 45 har sai fushin ɗan'uwanka ya huce daga gare ka, ya kuma manta abin da kayi masa. Daga nan zan aika a dawo da kai daga can. Don me zan rasa ku dukka a rana ɗaya? 46 Rebeka ta ce, "Na gaji da rayuwa saboda 'ya'yan Het. In Yakubu ya auri 'yanmata irin waɗannan mataye, waɗansu daga cikin 'yan matan ƙasar, wanne abu ne mai kyau zai zama a rayuwata?"