Sura 26

1 Sai aka yi yunwa a ƙasar, bayan wacce aka yi ta fari a kwanakin Ibrahim, Ishaku ya tafi wurin Abimelek, sarkin Filistiyawa a Gerar. 2 Sai Yahweh ya bayyana gare shi ya ce, "Kada ka gangara Masar; ka zauna a ƙasar dana ce ka zauna a ciki. 3 Ka zauna a wannan ƙasar, zan kasance tare da kai, in kuma albarkace ka; domin a gare ka da zuriyarka ne zan bayar da ƙasashen al'ummai, kuma zan cika alƙawarin dana yi wa Ibrahim mahaifinka. 4 Zan ruɓanɓanya zuriyarka kamar taurarin sama zan kuma bada waɗannan ƙasashe ga zuriyarka. Ta wurin al'ummarka dukkan ai'umman duniya zasu sami albarka. 5 Zan yi wannan domin Ibrahim ya yi biyayya da muryata ya kuma kiyaye dokokina, da farillaina, da shari'una. da ka'idodina." 6 Don haka Ishaku ya zauna a Gerar. 7 Da mutanen wurin suka tambaye shi game da matarsa, sai ya ce, "Ita 'yar'uwata ce". Ya ji tsoro ya ce, "Ita matata ce," saboda ya yi tunanin cewa, mutanen zasu kashe ni su ɗauke Rebeka domin ita kyakkyawa ce." 8 Bayan Ishaku ya daɗe a can, sai Abimelek sarkin Filistiyawa ya duba ta taga. Sai ya ga Ishaku na shafa Rebeka, matarsa. 9 Abimelek ya kira Ishaku gare shi ya ce, "Duba hakika ita matarka ce. Don me ka ce, ita 'yar'uwata ce'?" Ishaku yace da shi, "Saboda na yi tsammanin wani zai iya ya kashe ni don ya same ta." 10 Abimelek yace, "Me kenan ka yi mana? Da kuwa wani ya kwana da matarka cikin sauƙi, da kuma ka jawo mana laifi." 11 Sai Abimelek ya gargaɗi mutene ya ce, "Duk wanda ya taɓa mutumin nan ko matarsa hakika za a kashe shi." 12 Ishaku ya shuka hatsi a waccan ƙasar, ya kuma yi girbi a wannan shekara, ya sami riɓi ɗari, saboda Yahweh ya albarkace shi. 13 Mutumin ya azurta, ya dinga bunƙasa sosai har sai da ya yi girma sosai. 14 Yana da tumakai masu yawa da dabbobi, da iyalai masu yawa. Filistiyawa suka yi kishinsa. 15 To dukkan rijiyoyin da barorin mahaifinsa suka haƙa a kwanakin Ibrahim mahaifinsa, Filistiyawa suka cike su da ƙasa. 16 Abimelek yace da Ishaku, "Ka tafi ka ba mu wuri, domin ka fi mu ƙarfi." 17 Sai Ishaku ya bar garin ya koma Kwarin Gerar ya zauna a can. 18 Haka kuma Ishaku ya tone rijiyoyi na ruwa waɗanda aka haƙa a kwanakin Ibrahim mahaifinsa. Filistiyawa suka ɓata su bayan mutuwar Ibrahim. Ishaku ya kira rijiyoyin da ainihin sunan da mahaifinsa ya kira su. 19 Bayan barorin Ishaku sun yi tono a cikin kwarin, sai suka sami wata rijiya mai fitar da ruwa a can. 20 Makiyayan Gerar suka yi faɗa da makiyayan Ishaku suka ce, "Wannan ruwan namu ne." Domin haka Ishaku ya kira rijiyar "Esek" wato rikici, saboda sun yi rikici da shi. 21 Sai suka sake haƙa wata rijiyar, sai suka sake yin rikici akan itama wannan rijiyar, sai ya ba ta suna "Sitnah." 22 Sai ya bar wurin ya ƙara haƙa wata rijiyar, amma ba su yi rikici kan wannan ba. Don haka ya kira ta Rehobot, ya ce, "Yanzu Yahweh ya samar mana masauki, kuma za mu wadata a cikin ƙasar." 23 Sai Ishaku ya haura daga can zuwa Bayersheba. 24 Yahweh ya bayyana a gare shi a cikin wannan daren ya ce, "Ni ne Allah na Ibrahim mahaifinka. Kada ka ji tsoro, domin ina tare da kai zan kuma albarkace ka in ruɓanɓanya zuriyarka, saboda barana Ibrahim." 25 Ishaku ya gina bagadi ya yi kira bisa sunan Yahweh. A can ya kafa rumfarsa, barorinsa kuma suka haƙa rijiya. 26 Sai Abimelek ya je wurinsa daga Gerar, tare da Ahuzat, abokinsa, da Fikol, jagoran sojojinsa. 27 Ishaku yace da su, "Meyasa kuke zuwa gare ni, tun da yake kun ƙi ni, kun kuma kore ni daga wurinku?" 28 Sai suka ce, "Zahiri mun ga Yahweh na tare da kai. Shi yasa muka ga ya fi kyau a sami rantsuwa tsakaninmu, i, tsakaninmu da kai, To in ka yarda sai mu yi yarjejeniya da kai, 29 cewa ba zaka wahalshe mu ba, kamar yadda muka yi maka muka sallame ka cikin lumana, hakika Yahweh ya albarkace ka." 30 Sai ishaku ya shirya liyafa domin su, suka ci suka sha. 31 Suka tashi da asuba suka yi rantsuwar alƙawari da juna. Daga nan Ishaku ya sallame su, suka bar shi cikin salama. 32 A wannan ranar dai barorin Ishaku suka zo suka ba shi labari game da rijiyar da suka haƙa. Suka ce, Mun sami ruwa." 33 Ya kira rijiyar da suna Shiba, shi ya sa a ke kiran wannan birni da suna Bayersheba har ya zuwa yau. 34 Da Isuwa ya kai shekaru arba'in, ya auri mata mai suna Yudit 'yar Be'eri Bahitte, da kuma Basemat "yar Elon Bahitte. 35 Suka kawo baƙinciki ga Ishaku da Rebeka.