Sura 3

1 To maciji ya fi dukkan sauran dabbobin saura da Yahweh yayi wayau. Sai ya ce da macen, "Ko da gaske ne Allah yace ba zaku taɓa ci daga kowanne 'ya'yan itacen dake cikin lambun ba?" 2 Sai matar ta ce da macijin, "Ma iya ci daga cikin itatuwan lambun, 3 amma game da itacen dake tsakiyar lambun, Allah yace, 'Ba zaku ci shi ba, ba kuma zaku taɓa shi ba, in ba haka ba, zaku mutu."' 4 Sai maciji yace da macen, "Hakika ba zaku mutu ba. 5 Domin Allah ya san cewa a ranar da kuka ci idanunku zasu buɗe, zaku kuma zama kamar Allah, kuna sanin nagarta da mugunta." 6 Da matar ta duba ta ga itacen yana da kyau domin abinci, yana kuma ƙayatar da idanu, kuma itacen abin marmari ne yana sa mutum ya zama mai hikima, sai ta tsinki waɗansu daga cikin 'ya'yan ta ci shi. Sai ta bada waɗansu ga mijinta, shi kuma ya ci. 7 Idanun dukkan su biyun suka buɗe, sai suka gane tsirara su ke. Sai suka ɗinka ganyayyakin ɓaure suka yi wa kansu sutura. 8 Sai suka ji motsin Yahweh Allah ya na tafiya cikin lambun da sanyin yamma, domin haka mijin da matar suka ɓuya a cikin itatuwan lambun daga fuskar Yahweh Allah. 9 Sai Yahweh Allah ya kira mutumin yace da shi, "Ina ka ke?" 10 Mutumin yace "Na ji ka a cikin lambun, na kuma ji tsoro, domin tsirara na ke. Domin haka na ɓoye kaina." 11 Allah yace, "Wane ne ya faɗa maka cewa tsirara ka ke? Ko ka ci 'ya'yan itacen da na dokace ka kada ka ci daga cikinsa ne?" 12 Sai mutumin yace, "Macen daka ba ni ta kasance tare da ni, ta ba ni 'ya'yan itacen, na kuwa ci shi." 13 Yahweh Allah yace da matar, "Me ki ka yi kenan?" Sai macen ta ce, "Maciji ne ya yi mini ƙarya, na kuwa ci." 14 Yahweh Allah yace da maciji, "Saboda ka yi wannan, kai kaɗai ne la'ananne a cikin dukkan dabbobin saura da dukkan dabbobin sama. A kan cikinka za ka yi tafiya, kuma ƙasa za ka ci dukkan kwanakin ranka. 15 Zan sa magaftaka tsakaninka da matar, da kuma tsakanin zuriyarka da zuriyarta. Zai ƙuje kanka, kai kuma za ka ƙuje diddigensa." 16 Ga macen yace, "Zan ninka shan wuyarki sosai a samun 'ya'ya; a cikin shan wuya za ki haifi 'ya'ya. Duk marmarinki zai zama domin mijinki, amma zai yi mulkin ki." 17 Ga Adamu yace, "Domin ka saurari muryar matarka, ka ci daga cikin itacen da na dokace ka cewa, 'Kada ka ci daga cikinsa,' saboda kai na la'anta ƙasa; ta wurin aiki mai zafi za ka ci daga cikinta dukkan kwanakin ranka. 18 Za ta fitar da ƙaya da sarƙaƙƙiya domin ka, za ka kuma ci tsire-tsiren ƙasar. 19 Ta wurin zufarka za ka ci gurasa, har sai randa ka koma turɓaya, domin daga cikinta aka ciro ka. Domin kai ƙura ne, ƙura kuma za ka koma." 20 Mutumin ya kira sunan matarsa Hauwa ita ce mahaifiyar dukkan rayayyu. 21 Yahweh Allah ya yi wa Adamu da matarsa sutura ta fatu ya rufe su. 22 Yahweh Allah yace, "Yanzu mutumin ya zama kamar ɗaya daga cikinmu, yana sane da mugunta da nagarta. To yanzu ba za mu taɓa barinsa ya sa hannunsa, ya tsinka daga itacen rai ba, ya ci, ya kuma rayu har abada." 23 Saboda haka Yahweh Allah ya fitar da shi daga cikin lambun Aidin, domin ya noma ƙasa wanda daga ita aka ciro shi. 24 To sai Allah ya kori mutumin daga lambun, ya sa kerubim a gabashin lambun Aidin da kuma takobi mai walƙiya dake jujjuyawa ta kowanne fanni, domin su yi tsaron hanya ta zuwa itacen rai.