Sura 25

1 Sai Ibrahim ya auro wata mata mai suna Ketura. 2 Ta haifa masa Zimra, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak, da Shuwa. 3 Yokshan ya haifi Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Asiriya, da mutanen Letush, da mutanen Leyum. 4 'Ya'yan Midiyan sune Efa, Efer, Hanok, Abida, da Elda'ah. Duk waɗannan sune zuriyar Ketura. 5 Ibrahim ya mallaka duk abin da yake da shi ga Ishaku. 6 Duk da haka, a lokacin da yake raye ya ba da kyautai ga 'ya'yan ƙwaraƙwaransa ya aika su ƙasar gabas nesa da ɗansa Ishaku. 7 Waɗannan sune kwanakin shekarun rayuwar Ibrahim da ya yi shekaru, 175. 8 Ibrahim ya yi numfashinsa na ƙarshe ya mutu a cikin kyakkyawan tsufa, tsohon mutum mai cike da kuzari, sai aka tattara shi ga mutanensa. 9 Ishaku da Isma'ila, 'ya'yansa suka bizne shi a kogon Makfela, a filin Ifron ɗan Zohar Bahitte, wadda ke kusa da Mamre. 10 Wannan filin Ibrahim ya saya daga'ya'yan Het maza. A can aka bizne Ibrahim da matarsa Saratu. 11 Bayan mutuwar Ibrahim Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku, Ishaku ya zauna kusa da Beyer Lahai Roi. 12 To Waɗannan sune zuriyar Isma'ila ɗan Ibrahim, da Hajara Bamasariya baiwar Saratu, ta haifa wa Ibrahim. 13 Waɗannan sune sunayen 'ya'yan Isma'ila bisa ga tsarin haihuwarsu: Nebaiyot - shi ne ɗan fari na Isma'ila, da Kedar, da Adbe'el, da Mibsam, 14 da Mishma, da Massa, 15 Hadad, da Tema, da Yetur, da Nafish, da Kedema. 16 Waɗannan su ne 'ya'yan Isma'ila, kuma waɗannan sune sunayensu bisa ƙauyukansu, suna kuma da sarakuna sha biyu bisa ga kabilarsu. 17 Waɗannan su ne shekarun rayuwar Isma'ila, shekaru, 137 ya yi numfashinsa na ƙarshe sa'an nan ya mutu, sai aka tattara shi ga mutanensa. 18 Sun yi rayuwa daga Habila zuwa Ashur, wadda take kusa da Masar, ɗaya kuma ya nufi Asiriya. Sun yi zaman tankiya da juna. 19 Waɗannan su ne al'amura game da Ishaku, ɗan Ibrahim: Ibrahim ya haifi Ishaku. 20 Ishaku nada shekaru arba'in a lokacin da ya ɗauki Rebeka a matsayin matarsa, 'yar Betuwel mutumin Aramiya ta Faddan Aram, 'yar'uwar Laban na Aramiya. 21 Ishaku ya yi addu'a ga Yahweh domin matarsa saboda ba ta da ɗa, Yahweh kuma ya amsa addu'arsa, Rebeka matarsa kuma ta yi juna biyu. 22 'Ya'yan na ta fama tare tun daga cikinta, sai ta ce, "Meyasa wannan ke faruwa da ni?" Ta je ta tambayi Yahweh game da haka. 23 Yahweh yace da ita, "Al'umma biyu ce a mahaifarki, mutane biyu kuma zasu rabu daga gare ki. Ɗaya jama'ar za ta fi ɗayar ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin." 24 Da lokacin haihuwarta yayi, sai ta kasance da 'yan biyu a mahaifarta. 25 Na farkon ya fito da gargasa a ko'ina kamar tufafin gashi. Suka kira sunansa Isuwa. 26 Bayan haka, ɗan'uwansa ya fito hannuwansa na‌ riƙ‌e da diddigen Isuwa. Sai aka kira shi Yakubu. Ishaku na da shekaru sittin lokacin da matarsa ta haifa masa su. 27 Samarin suka yi girma, Isuwa ya zama shahararren mafarauci mai yawo a saura; amma Yakubu mai shiru-shiru ne, wanda ya kashe lokacinsa cikin runfofi. 28 Sai ishaku ya ƙaunaci Isuwa domin yakan ci namomin jejin da ya harbo, amma Rebeka ta ƙaunaci Yakubu. 29 Yakubu ya shirya ɗan dage-dage. Isuwa ya zo daga saura, ya kuma raunana saboda yunwa. 30 Isuwa yace da Yakubu, "Ka ciyar da ni da dage-dagenka mana. Ina roƙonka ƙarfina ya ƙare!" Shiyasa aka kira sunansa Idom. 31 Yakubu yace, "Da farko ka sayar mani da matsayinka na ɗan fari tukuna." 32 Isuwa yace, "Duba, Na kusa mutuwa. Wanne amfani ne matsayin ɗan fari ke da shi a gare ni?" 33 Yakubu yace, "Da farko sai ka rantse mani" ta haka Isuwa ya yi rantsuwa kuma ta haka Isuwa ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yakubu. 34 Yakubu ya ba Isuwa dage-dagen wake da gurasa. Ya ci ya sha, daga nan ya tashi ya tafi abinsa. Ta wannan hali Isuwa ya banzantar da matsayinsa na ɗan fari.