Sura 24

1 Ya zamana kuma Ibrahim ya tsufa ainun, kuma Yahweh ya albarka ce shi a cikin komai. 2 Sai Ibrahim yace da baransa, wanda ya fi daɗewa da kuma ke kula da komai da ya mallaka, ya ce "Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata, 3 zan sa ka ka rantse da Yahweh, Allah na sama da kuma Allah na duniya, cewa ba zaka auro wa ɗana mata daga cikin Kan'aniyawan da nake zama a cikinsu ba. 4 Amma zaka je cikin ƙasata da dangina ka auro wa ɗana Ishaku mata daga can." 5 Sai baran yace da shi, "To yaya kenan, in matar ta ce ba za ta biyo ni zuwa wannan ƙasar ba fa? Ko ya zama tilas in mayar da ɗanka zuwa ƙasar da ka baro?" 6 Ibrahim yace da shi, "Ka tabbata cewa ba ka komar da ɗana can ba! 7 Yahweh Allah na sama, wanda ya ɗauko ni daga gidan mahaifina da kuma ƙasar dangina, wanda kuma ya yi mini tabbataccen alƙawari cewa, 'Ga zuriyarka zan bada wannan ƙasa,' zai aiko mala'ikansa a gabanka, kuma zaka samo wa ɗana mata daga can. 8 Amma in matar ba ta son ta biyo ka, to ka kuɓuta daga rantsuwata, kada ka komar da ɗana can," 9 Sai baran ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyoyin Ibrahim shugabansa, ya yi masa rantsuwa game da wannan al'amari. 10 To sai baran ya ɗauki raƙuma goma na shugabansa ya tafi. Haka nan ya ɗauki duk waɗansu kyaututtuka da suka kamata daga wurin shugabansa ya tafi da su yankin Aram Naharaim zuwa birnin Nahor. 11 Ya sa raƙuman suka kwakkwanta a gefen rijiyar ruwa. Da yamma ne daidai lokacin da mata ke fita ɗiban ruwa. 12 Daga nan sai ya ce, "Yahweh, Allah na shugabana Ibrahim, ka ba ni nasara a yau ka kuma nuna amintaccen alƙawarinka ga shugabana Ibrahim. 13 Duba yanzu ina tsaye a bakin ƙoramar ruwa, kuma 'yan'matan mutanen birnin suna fitowa domin su ɗibi ruwa. 14 Ka sa abin ya kasance kamar haka. In na ce da budurwar ina roƙon ki ki saukar da abin ɗiban ruwanki domin in sha; sai kuma ta ce da ni, ka sha, zan kuma shayar da raƙumanka ma; to bari ta zama matar daka nufa ta zama matar bawanka Ishaku. Da haka zan sani cewa ka nuna amintaccen alƙawarinka ga shugabana." 15 Sai ya zamana kafin ma ya gama magana sai ga Rebeka ta zo da abin ɗiban ruwanta a kafaɗarta. Rebeka 'yar Betuwel ce ɗan Milka, matar Nahor, ɗan'uwan Ibrahim. 16 Budurwar kyakkyawa ce kuma ba ta ɓata budurcinta ba. Ba mutumin da ya taɓa kwana da ita. Sai ta tafi ƙoramar ta cika abin ɗiban ruwanta, ta hauro. 17 Sai baran ya yi gudu domin ya gamu da ita ya ce, "Ina roƙo ki sam mani ruwa in ɗan sha daga cikin abin ɗiban ruwanki." 18 Ta ce ya shugabana ka sha sai ta yi sauri ta sauke abin ɗiban ruwan ƙasa a hannunta ta ba shi ya sha. 19 Bayan ta gama ba shi ya sha, sai ta ce, "Zan ɗebowa raƙumanka ma su sha har sai sun kammala sha." 20 Sai ta yi sauri ta juye abin ɗebo ruwan, ta yi gudu ta sake komawa rijiyar domin ta ɗebo ruwa domin dukkan raƙumansa. 21 Sai mutumin ya dube ta a natse domin ya gani ko Yahweh ya ba tafiyarsa nasara ko kuwa a'a. 22 Bayan raƙuman sun gama shan ruwan, sai mutumin ya ciro zoben zinariya na hanci mai nauyin rabin ma'auni, da ƙarau guda biyu na azurfa na sawa a dantse wanda ya kai nauyin ma'auni goma, 23 sai ya tambaya, "Ke "yar wane ne? Ina roƙon ki ki faɗa mini, ko akwai masauki a gidan mahaifinku da za mu kwana?" 24 Ta ce da shi, "Ni 'yar Batuwel ce ɗan Milka wanda ta haifawa Nahor." 25 Ta kuma ce da shi muna kuma da ciyawa da abincin dabbobi da kuma ɗaki domin ku kwana." 26 Sai mutumin ya sunkuya ƙasa ya yi sujada ga Yahweh. 27 Ya ce, "Albarka ta tabbata ga Yahweh, Allah na shugabana Ibrahim, wanda bai yashe da alƙawarinsa mai aminci ba da kuma amincinsa ga shugabana. Ni da kaina Yahweh ya bi da ni kai tsaye zuwa gidan dangin shugabana." 28 Sai budurwar ta yi gudu ta je ta faɗa wa iyalin gidan mahaifiyarta duk abin da ya faru dangane da waɗannan al'amura. 29 Rebeka kuma tana da ɗan'uwa, sunansa Laban. Sai Laban ya ruga zuwa wurin mutumin wanda ke can kan hanyar ƙoramar. 30 Da ya ga wannnan zobe na hanci da ƙarau na dantse a dantsen 'yar'uwarsa, kuma bayan ya ji duk abin da Rebeka 'yar'uwarsa ta faɗa, "Wannan shi ne abin da mutumin ya ce da ni," sai ya tafi wurin mutumin, sai ga shi a tsaye a gefen raƙuma a wurin ƙoramar. 31 Sai Laban yace, "Zo, kai mai albarka na Yahweh. Meyasa kake tsayuwa a waje? Na shirya gida da kuma wuri domin raƙuman." 32 Sai mutumin ya zo gidan ya kuma sauke wa raƙuman kaya. Sai aka ba raƙuman ciyawa da abincin dabbobi aka kuma tanadi ruwa domin ya wanke ƙafafunsa da kuma na mutanen dake tare da shi. 33 Suka kawo masa abinci domin ya ci, amma ya ce, "Ba zan ci ba sai na faɗi abin da zan faɗa. "Sai Laban yace to faɗi abin da zaka faɗa." 34 Ya ce, "Ni baran Ibrahim ne. 35 Yahweh ya albarkaci shugabana sosai ya kuma yi girma sosai. Ya ba shi garkuna da dabbobi da zinariya da azurfa, da bayi maza da mata da raƙuma da jakuna. 36 Saratu matar shugabana ta haifi ɗa ga shugabana a lokacin da ya tsufa, ya kuma bayar da duk abin da ya mallaka gare shi. 37 Shugabana ya sa na rantse, cewa, 'Ba za ka auro wa ɗana mata daga cikin 'yanmatan Kan'aniyawa ba, waɗanda a ƙasarsu na yi gidana. 38 Maimakon haka dole ka je wajen dangin mahaifina, cikin 'yan'uwana ka samo wa ɗana matar aure.' 39 Na ce da shugabana, in a ce matar ba zata biyo ni ba fa.' 40 Amma ya ce da ni, Yahweh wanda nayi tafiya a gabansa, zai aiko mala'ikansa ya kasance tare da kai ya kuma baka nasara bisa tafiyarka, domin ka auro wa ɗana mata daga cikin dangina da kuma iyalin mahaifina. 41 Amma zaka kuɓuta daga rantsuwata in ka zo wurin 'yan'uwana in ba su baka ita ba. To zaka kuɓuta daga rantsuwata.' 42 To da na kawo wurin ƙorama, na ce, 'Ya Yahweh, Allah na shugabana Ibrahim, ina roƙon ka, in har ka so ka ba tafiyata nasara- 43 gani nan a tsaye a bakin ƙorama-ka sa budurwar da ta zo ɗiban ruwa, wato macen da zan ce, "Ina roƙo ki ɗan san mani ruwa in sha daga abin ɗiban ruwanki," 44 macen da ta ce da ni, "Sha, zan kuma shayar da raƙumanka"_Bari ta zama macen da kai, Yahweh, ka zaɓa domin ɗan shugabana.' 45 Tun ma kafin in gama magana a cikin zuciyata, sai ga, Rebeka ta zo da abin ɗiban ruwanta a kafaɗarta sai ta gangara ƙoramar ta ɗebo ruwa. Sai na ce da ita, 'Ina roƙo ki bani ruwa in sha.' 46 Sai ta yi sauri ta sauko da abin ɗiban ruwan daga kafaɗarta ta ce, 'Ka sha, zan kuma shayar da raƙumanka.' Sai na sha, ta kuma shayar da raƙuman. 47 Na tambaye ta cewa, 'Ke 'yar wane ne?' Ta ce, 'Yar Betuwel, ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.' Daga nan sai na sa zoben a hancinta da kuma ƙarau a damtsenta. 48 Sai na sunkuya na yi sujada ga Yahweh, na albarkaci Yahweh Allah na shugabana Ibrahim, wanda ya bishe ni a madaidaiciyar hanya domin in sami 'yar dangin shugabana domin ɗansa. 49 Yanzu kuma, in kuna shirye ku nuna zumunci mai aminci da amana, ku faɗa mini. Amma in ba haka ba, ku faɗa mini, domin in bi dama ko hagu." 50 Sai Laban da Betuwel suka amsa suka ce, Al'amarin daga Yahweh ya zo; ba zamu iya ce maka ya yi kyau ko bai yi kyau ba. 51 Duba Rebeka na gabanka. Ɗauke ta ku tafi, domin ta zama matar ɗan shugabanka, kamar yadda Yahweh ya faɗa." 52 Da baran Ibrahim ya ji maganarsu, sai ya sunkuyar da kansa ƙasa ga Yahweh. 53 Sai baran ya fito da kayayyaki na zinariya da azurfa da sutura ya miƙa su ga Rebeka. Hakanan ya bada kyautai masu daraja ga ɗan'uwanta da kuma mahaifiyarta. 54 Daga nan shi da mazajen dake tare da shi suka ci, suka sha. Suka kwana har gari ya waye, bayan sun tashi da safe, ya ce "Ku sallame ni zuwa gun shugabana." 55 Ɗan'uwanta da mahaifiyarta suka ce, "Bari budurwar ta ɗan yi waɗansu 'yan kwanaki kamar goma tukuna. Bayan nan za ta iya ta tafi." 56 Amma ya ce da su kada ku hana ni da yake Yahweh ya sa tafiyata ta yi nasara. Ku sallame ni domin in koma wurin shugabana." 57 Suka ce za mu kira budurwar mu tambaye ta." 58 Sai suka kira Rebeka suka tambaye ta, "Za ki tafi tare da wannan mutumin?" Ta amsa "zan tafi." 59 Sai suka aika 'yar'uwarsu Rebeka, tare da baranyarta, a cikin tafiyarta tare da baran Ibrahim da mazajensa. 60 Suka albarkaci Rebeka, suka ce da ita, "Yar'uwarmu, muna addu'a ki zama uwar dubun dubbai goma, da ma zuriyarki ta mallaki ƙofar maƙiyansu." 61 Sai Rebeka ta tashi, ita da barorinta mata suka hau raƙuma, suka bi mutumin. Da haka baran ya ɗauki Rebeka ya yi tafiyarsa. 62 Ya zamana Ishaku na zama a Negeb, ya dawo kenan daga Beyerlahairoi. 63 Ishaku ya fita domin yin nazari a saura da yammaci. Da ya duba tudu, ya hanga, sai ya ga raƙuma na tafe! 64 Rebeka ta duba, da ta ga Ishaku sai ta diro daga kan raƙumin. 65 Ta ce da baran, "Wane ne wancan dake tafiya a cikin saura domin ya tarbe mu?" Baran yace, "'Shugabana ne." Sai ta ɗauki gyale ta yi lulluɓi. 66 Baran ya zaiyana wa Ishaku dukkan abin da ya yi. 67 Sai Ishaku ya kawo ta rumfar mahaifiyarsa Saratu ya ɗauki Rebeka, ta zama matarsa, ya kuma ƙaunace ta. Da haka Ishaku ya ta'azantu bayan mutuwar mahaifiyarsa.