Sura 23

1 Saratu ta rayu tsawon shekaru ɗari da ashirin da bakwai. Waɗannan sune shekarun Saratu. 2 Saratu ta mutu a Kiriyat Arba wato Hebron, a ƙasar Kan'ana. Ibrahim ya yi makoki da kuka domin Saratu. 3 Sai Ibrahim ya tashi ya bar wurin da matarsa ta mutu, ya yi magana da 'ya'yan Het, cewa. 4 "Ni bãƙo ne a cikin ku Ina roƙo ku bani mallakar wurin maƙabarta a cikinku domin in bizne matattuna." 5 Sai 'ya'yan Het suka amsa wa Ibrahim cewa, 6 "Ka saurare mu shugabana. Kai yariman Allah ne a cikin mu. Bizne matattunka a duk inda ka zaɓa a maƙabartunmu, ba wanda zai hana maka maƙabartarsa domin ka bizne matattunka." 7 Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna wa mutanen ƙasar, ga "ya'yan Het. 8 Ya yi musu magana cewa, "In kun yarda cewa in bizne matacciyata, sai ku saurare ni ku roƙi Ifron ɗan Zohar domi na. 9 Ku tambaye shi ya sayar mini da kogon Makfela, wadda ya mallaka, wadda yake a ƙarshen filinsa. Domin cikakken farashi ya kuma sayar mini da shi a gaban mutane domin ya zama mallakata, da maƙabarta." 10 Ifron kuma na zaune a cikin 'ya'yan Het, sai Ifron Bahitte ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan 'ya'yan Het maza da kuma duk waɗanda suka zo ƙofar birninsa, cewa, 11 "A'a shugabana, ka saurare ni. Na baka filin da kuma kogon dake cikinsa. Na baka shi a gaban 'ya'yan mutanena maza. Na baka shi domin bizne matacciyarka." 12 Sai Ibrahim ya sunkuyar da kansa ƙasa a gaban mutanen ƙasar. 13 Ya yi magana da Ifron a kunnen mutanen ƙasar cewa. "Amma in ka amince, inka yarda ka saurareni. Zan biya kuɗin filin. Ka karɓi kuɗi daga wuri na, ni kuma zan bizne mattaciyata a can." 14 Ifron ya amsa wa Ibrahim, da cewa, 15 "Ina roƙo, ya shugabana, ka saurare ni.‌ Ɗan yankin ƙasa na shekel ɗari huɗu na azurfa, mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka bizne mamaciyarka." 16 Ibrahim ya saurari Ifron, ya auna shekel ɗari huɗu kamar yadda Ifron ya ambata a kunnuwan dukkan 'ya'yan Het maza, mudu ɗari huɗu na zinariya, bisa ga mizanin ma'aunin fatake. 17 Domin haka filin Ifron dake a Makfela wanda ke gaban Mamre, wato da filin da kogon dake cikinsa, da duk itatuwan dake cikin filin, da dukkan iyakarsa, 18 aka ba Ibrahim tawurin sayarwa a gaban 'ya'yan Het maza, da kuma duk waɗanda suka zo ƙofar birninsa. 19 Bayan wannan Ibrahim ya bizne Saratu matarsa a cikin kogon filin Makfela, wanda ke gaba da Mamre wato Hebron, a cikin ƙasar Kan'ana. 20 Domin haka da filin da kogon dake cikinsa aka miƙa su ga Ibrahim daga 'ya'yan Het maza domin ya zama maƙabarta.