Sura 22

1 Sai ya zamana bayan waɗannan abubuwa Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce da shi, "Ibrahim" Ibrahim yace, "Ga ni nan," 2 Sai Allah yace, "Ka ɗauki ɗanka, tilon ɗanka, wanda kake ƙauna, Ishaku, sai ku je ƙasar Moriya. A can za ka miƙa shi baiko na ƙonawa akan ɗaya daga cikin duwatsun dake can, wanda zan faɗa maka game da shi." 3 Sai Ibrahim ya tashi da asuba ya ɗaura wa jakinsa sirdi, ya kuma ɗauki biyu daga cikin matasan mazajensa tare da shi, haɗe kuma da Ishaku ɗansa. Ya sassari itace domin baiko na ƙonawa, daga nan ya kama hanyarsa zuwa inda Allah ya faɗa masa. 4 A rana ta uku Ibrahim ya duba sama sai ya hangi wurin daga nesa. 5 Sai Ibrahim yace da matasansa, "Ku tsaya nan da jakin, ni da yaron zamu haura can. Za mu yi sujada daga nan sai mu dawo wurinku." 6 Sai Ibrahim ya ɗauki itace domin hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa Ishaku ɗansa. Sai ya ɗauki wuƙa da wuta a hannunsa; sai kuma suka tafi tare. 7 Ishaku ya yi magana da Ibrahim mahaifinsa ya ce, "Babana," sai ya ce, "Ga ni nan ɗana." Ya ce, Ga wuta anan da itace, amma ina ɗan ragon baikon ƙonawa?" 8 Ibrahim yace, "Ɗana Allah da kansa zai tanada ɗan rago domin baikon ƙonawa." Sai suka ci gaba da tafiya tare su dukka. 9 Sa'ad da suka zo wurin da Allah ya faɗa masa, Sai Ibrahim ya gina bagadi a can ya zuba itace a kansa. Sai ya ɗaure ɗansa Ishaku, ya ɗora shi akan bagadin bisa itacen. 10 Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauko wuƙa domin ya yanka ɗansa. 11 Sai mala'ikan Yahweh ya kira shi daga sama ya ce, "Ibrahim, Ibrahim!" sai ya ce, "Ga ni nan." 12 Ya ce, "Kada ka ɗora hannunka a kan yaron, kar ka yi duk wani abu da zai cutar da shi, domin yanzu na sani kana tsoron Allah, ganin cewa ba ka hana mini ɗanka ba, tilon ɗanka." 13 Ibrahim ya duba sama, sai ga ɗan rago a sarƙafe da ƙahonsa. Ibrahim ya ɗauki ɗan ragon ya miƙa shi baiko na ƙonawa a maimakon ɗansa. 14 Saboda haka Ibrahim ya kira wurin, "Yahweh zai tanada," haka kuma ake kiran wurin har yau,"A kan tsaunin Yahweh za a tanada shi." 15 Mala'ikan Yahweh ya kira Ibrahim daga sama a karo na biyu 16 ya ce - wannan shi ne furcin Yahweh - na yi rantsuwa da kaina cewa da yake ka yi wannan abu, ba ka hana ɗanka ba tilon ɗanka, 17 Hakika zan albarkace ka zan kuma ruɓanɓanya zuriyarka kamar taurarin sammai, kamar kuma yashin dake gaɓar teku; zuriyarka kuma zasu mallaki ƙofar maƙiyansu. 18 Ta wurin tsatsonka za a albarkaci dukkan al'ummar duniya, saboda ka yi biyayya da muryata." 19 Sai Ibrahim ya koma wurin barorinsa, suka tafi Beyarsheba tare sai ya zauna a Beyarsheba. 20 Ya zamana bayan waɗannan abubuwa sai, aka ce da Ibrahim "Milka ta haifi 'ya'ya, haka kuma ɗan'uwanka Nahor." 21 Su ne Uz ɗansa na fari, Buz shi ne ɗan'uwansa, Kemuwal shi ne mahaifin Aram, da 22 Kesed da Hazo, da Fildash da Yidlaf da Betuwel. 23 Betuwel ya haifi Rebeka. Waɗannan sune 'ya'ya takwas da Milka ta haifa wa Nahor, ɗan'uwan Ibrahim. 24 Ƙwarƙwararsa mai suna Reuma ita ma ta haifi Tebah da Gaham Tahash da Ma'aka.