Sura 21

1 Yahweh ya saurari Saratu kamar yadda ya ce zai yi, Yahweh kuwa ya yi wa Saratu kamar yadda ya alƙawarta. 2 Saratu kuwa ta yi juna biyu ta haifa wa Ibrahim ɗa a cikin kwanakin tsufansa, a daidai lokacin da Yahweh ya yi masa magana. 3 Ibrahim kuma ya raɗa wa ɗansa suna, wato wannan ɗa da aka haifa masa, wannan da Saratu ta haifa masa wato Ishaku. 4 Ibrahim ya yi wa ɗansa Ishaku kaciya da yayi kwana takwas, kamar dai yadda Allah ya umarce shi. 5 Ibrahim na da shekaru ɗari a lokacin da aka haifa masa Ishaku. 6 Saratu ta ce, "Allah ya sa ni dariya, duk wanda ya ji zai yi dariya tare da ni." 7 Wane ne zai ce da Ibrahim cewa Saratu za ta yi masa renon 'ya'ya, kuma duk da haka na haifa masa ɗa a kwanakin tsufansa!" 8 Yaron ya yi girma aka yaye shi, Ibrahim ya yi babbar liyafa a ranar da aka yaye Ishaku. 9 Saratu ta ga ɗan Hajara Bamasariya, da ta haifa wa Ibrahim, na ba'a. 10 Saboda haka ta ce da Ibrahim, "Ka kori wannan baiwar matar da ɗanta: domin ɗan wannan baiwar ba zai ci gãdo, tare da ɗana Ishaku ba." 11 Wannan abin ya yi wa Ibrahim zafi a rai saboda ɗansa. 12 Amma Allah yace da Ibrahim, "Kada ka damu saboda yaron, da kuma saboda wannan matar baiwarka. Ka saurari kalmominta kan duk abin da ta faɗa maka kan wannan al'amari, saboda ta wurin Ishaku ne za a kira zuriyarka. 13 Hakanan zan sa ɗan baiwar matar ya zama al'umma, domin shi zuriyarka ne." 14 Ibrahim ya ta shi da asuba, ya ɗauki gurasa da goran ruwa, ya ba da shi ga Hajara ya ɗora shi a kafaɗarta. Ya ba ta ɗan ya sallame ta ta tafi. Ta tafi ta yi ta yawo cikin jejin Beyersheba. 15 Da ruwan da ke cikin goran ruwan ya ƙare, sai ta yashe da ɗan a gindin wasu ciyayi. 16 Sai ta tafi ta zauna can nesa dai-dai harbin kibiya, domin ta ce, "Kada in ga mutuwar ɗana." Da ta zauna daura da shi sai ta ta da murya ta yi kuka. 17 Allah ya ji kukan ɗan, sai mala'ikan Allah ya kira Hajara daga can sama, ya ce da ita, "Me ke damun ki, Hajara? Kada ki ji tsoro, domin Allah ya ji kukan ɗan a inda yake. 18 Tashi ki ɗauki yaron, ki ƙarfafa shi, domin zan maishe shi babbar al'umma." 19 Sai Allah ya buɗe idanunta, sai ta ga rijiyar ruwa. ta je ta cika gorar da ruwa, ta ba ɗan ya sha. 20 Allah na tare da ɗan, ya kuma yi girma. Ya yi rayuwa cikin jeji sai ya zama mafarauci. 21 Ya yi rayuwa a jejin Faran, mahaifiyarsa kuma ta aura masa mata daga ƙasar Masar 22 Sai ya zamana a lokacin da Abimelek da Fikol shugaban sojojinsa ya yi magana da Ibrahim, cewa, "Allah na tare da kai a cikin dukkan al'amuranka. 23 Yanzu sai ka rantse mini cewa ba zaka yi mini ƙarya ba, haka kuma 'ya'yana, da zuriyata. Ka nuna mini da kuma ƙasar da kake zaune a ciki irin wannan alƙawari mai aminci da na nuna gare ka." 24 Ibrahim yace "Na rantse." 25 Ibrahim kuma ya miƙa kukansa ga Abimelek game da rijiyar ruwa da bayin Abimelek su ka ƙwace daga wurinsa. 26 Abimelek yace "Ban san wanda ya yi wannan abu ba. Ba ka faɗa mini ba tuntuni; Ban ji al'amarin ba sai yau." 27 Sai Ibrahim ya ɗauki tumaki da shanu ya ba Abimelek, su biyun suka yi yarjejeniya. 28 Sai Ibrahim ya ware raguna bakwai na garken da kansu. 29 Abimelek yace da Ibrahim, "Mene ne ma'anar waɗannan matan tumakin daka shirya su da kansu?" 30 Ya amsa, waɗannan matan tumakin guda bakwai zaka karɓa daga hannuna, domin su zama shaida domina, cewa ni na haƙa wannan rijiya." 31 Sai ya kira wannan wurin Biyasheba, saboda a can ne dukkan su suka yi rantsuwa. 32 Suka yi yarjejeniya, Daga nan sai Abimelek da Fikol, shugaban sojojinsa, ya koma ƙasar Filistiyawa. 33 Ibrahim ya dasa itacen sabara a Biyasheba. a can ya yi sujada ga Yahweh, Allah madawwami. 34 Ibrahim ya zauna a matsayin baƙo a ƙasar filistiyawa na kwanaki masu yawa.