Sura 20

1 Ibrahim ya bar wurin ya gangara zuwa Negeb, ya zauna tsakanin Kadesh da Shur. Shi baƙo ne mazaunin Gerar. 2 Ibrahim yace game kuma da Saratu matarsa, "Ita 'yar'uwata ce" Sai Abimelek sarkin Gerar ya aika mazajensa suka ɗauko Saratu. 3 Amma Allah ya zo wurin Abimelek a mafarki da duhu, ya ce da shi, "Duba kai mataccen mutum ne saboda matar daka ɗauko, domin ita matar mutumin ce." 4 Abimelek kuma bai kusance ta ba ya ce, "Ubangiji ko zaka kashe har ma al'umma mai adalci? Ashe ba shi da kansa ne ya ce da ni 'ita 'yar'uwataba ce?' 5 Har ma ita da kanta ta faɗa, cewa 'Shi ɗan'uwana ne.' Na yi wannan bisa nagartar zuciyata, da kuma rashin laifofin hannuwana." 6 Sai Allah yace da shi a cikin mafarki, I nima na sani ka yi haka ne bisa ga nagartar zuciyarka, Ni ma kuma na hana ka yi mini zunubi. Saboda haka ne ban bar ka ka taɓa ta ba. 7 Saboda haka ka mayar wa mutumin matarsa domin shi annabi ne. Zai yi maka addu'a kuma za ka rayu. Amma in ba ka mayar da ita ba, ka sani tabbas kai da dukkan abin da ke naka zaku hallaka." 8 Abimelek ya tashi da asuba ya kira dukkan bayinsa gare shi. Ya faɗa musu duk waɗanna abubuwa, sai mazajensa suka firgita. 9 Sai Abimelek ya kira Ibrahim yace da shi, "Me kenan ka yi mana? Yaya nayi maka laifi, da ka jawo wa mulkina da ni kaina wannan zunubi? Ka yi mini abin da bai kamata a yi ba." 10 Abimelek yace da Ibrahim, "Meyasa ka yi wannan abin?" 11 Ibrahim yace, domin na yi tsammanin cewa hakika babu tsoron Allah a wannan wurin, kuma zasu kashe ni saboda matata.' 12 Bayan haka kuma hakika ita 'yar'uwata ce, 'yar mahaifina ce, amma ba 'yar mahaifiyata ba, sai kuma ta zama matata. 13 Lokacin da Allah ya sa na bar gidan mahaifina in yi tafiya daga wannan wuri zuwa wancan wuri, na ce da ita dole ne ki nuna mini wannan aminci a matsayin matata: A duk inda muka je ki faɗi haka game da ni, "Shi ɗan'uwana ne."" 14 Sai Abimelek ya kwashi tumaki da takarkari da maza da mata na bayi ya bada su ga Ibrahim. Daga nan ya mayar da Saratu, matar Ibrahim a gare shi. 15 Abimelek yace, "Duba, wannan ƙasar tawa tana gabanka. Ka zauna a duk inda ya yi maka kyau." 16 Ga Saratu kuma ya ce, duba, na ba ɗan'uwanki azurfa dubu. Wannan domin ya shafe duk wani laifi dana yi maku ne a fuskarku dukka, da kuma a gaban kowa da kowa, hakika kun yi abin da ke dai-dai." 17 Sai Ibrahim ya yi addu'a sai Allah ya warkar da Abimelek, da matarsa, da bayinsa mata domin su iya haifar 'ya'ya. 18 Domin Yahweh yasa dukkan matan gidan Abimelek su zama marasa haihuwa baki ɗaya, Saboda Saratu matar Ibrahim.